Sabbin Katinan Zabe 13m Muka Buga —INEC


Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) na bincike kan zargin jami’anta da karbar na goro a aikin rabon katin zabe da ke gudana.

Hukumar ta kara da cewa ta buga sabbin katinan zabe miliyan 13 da dubu 868 da 441 bayan kammala aikin rajistar sabbin masu zabe.

Da yake sanar da hakan, Kwamishinan INEC na Kasa kan Wayar da Masu Zabe da Yada Labarai, Festus Okoye, ya ce, “Hukumar ta damu bayan samun korafe-korafe kan nuna fifiko a wasu wuraren rabon katin.

“Duk halastattun masu rajista na da ’yancin karbar katinsu domin kada kuri’a a ranar zabe a wuraren da suka yi rajista.”

“Domin kawar da shakku, sabbin katunan zabe miliyan 3 da dubu 868 da 441 INEC ta buga da suka hada da na sabbin wadanda suka yi rajista da wadanda suka sauya wurin zabe da kuma wadanda aka sabunta katinsu.”

Okoye ya sanar cewa hukumar ta kara lokacin rabon katin zuwa ranar 29 ga watan Janairu da muke ciki, daga karfe 9 na safe zuwa 3 na rana, har da ranakun Asabar da Lahadi.

Hukumar ta kuma umarci jami’anta masu aikin rabon katin da su tattara duk wani korafi rashin buga kati zuwa ga shugabanninsu a jihohi domin daukar matakin da ya dace.

(AMINIYA)

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki