Posts

Showing posts with the label Hadin Gwiwa

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Jaddada Aniyarta Na Hada Gwiwa Da Majalisar Dokoki Ta Kano

Image
Laminu Rabi’u Danbappa, ya bayyana hakan ne yau a lokacin da ya karbi bakuncin kwamitin majalisar kan harkokin aikin hajji a ofishinsa wanda ya kai ziyarar ban girma ga hukumar.   A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu,Laminu ya kara da cewa Hukumar Jin Dadin Alhazai, tana iya yiwuwa ne kawai idan aka hada hannu da juna domin kare abin da aka damka wa alhazai. A nasa bangaren, shugaban kwamitin alhazai na majalisar, kuma dan majalisar wakilai mai wakiltar karamar hukumar, Honarabul Sarki Aliyu Daneji, ya ce sun kasance a hukumar alhazai domin nuna fuskokinsu a matsayinsu na mambobin kwamitin daga majalisar dokokin jiha. Sarki Aliyu Daneji, yayi kira ga ma’aikatan gudanarwa da su bada hadin kai domin cimma burin da aka sanya a gaba. A nasa jawabin dan majalisar wakilai mai wakiltar karamar hukumar Dala a majalisar dokokin jiha Hon Lawan Hussaini Cediyar yan’gurasa ya shawarci hukumar alhaza

Gwamnatin Kano za ta hada gwiwa da Jami’o’i masu zaman kansu don bunkasa ci gaban dan Adam – Gwamna Abba Kabir

Image
Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce jihar za ta hada hannu da manyan jami'o'i masu zaman kansu a ciki da wajen kasar nan domin ci gaban bil'adama. A sanarwar da babban sakataren Yada labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, tace Gwamnan ya bayyana hakan  a gidan gwamnatin Kano a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban kungiyar jami’o’in Afirka masu zaman kansu Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo. Mai Martaba Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana Farfesa Gwarzo a matsayin hamshakin dan kasuwa a fannin ilimi wanda kuma ke kokarin inganta makarantun gaba da sakandare duk da karancin jarin da yake samu. Gwamnan wanda ya yaba da kokarin Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo a kokarinsa na samar da ilimin jami’a mai zaman kansa a farashi mai rahusa, ya mika hanunsa da jami’o’in jihar Kano guda biyu. Tun da farko, Farfesa Gwarzo ya ce ya ziyarci gwamnan da mataimakinsa ne domin gabatar da takardar shaidar wasu jami’o’i masu zaman kansu guda biyu da ya sa