Search This Blog

Showing posts with label Burtaniya. Show all posts
Showing posts with label Burtaniya. Show all posts

Wednesday, 23 August 2023

Birtaniya Ta Gurfanar Da Diezani A Gaban Kotu Kan Zargin Almundahana

Kasar Birtaniya ta gurfanar da tsohuwar Ministar Man Fetur ta Najeriya, Diezani Alison-Madueke a gaban kotu kan zargin rashawa lokacin da take Minista.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa ’yan sandar kasar sun ce sun maka ta a kotun ne saboda suna zargin ta karbi cin hanci a wasu kwangilolin man fetur da iskar gas.

Diezani, mai shekara 63 a duniya, na daya daga cikin kusoshi a gwamnatin tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan.

A zamanin mulkin tsohon Shugaban, Diezani ta rike mukamin Ministar Mai ta Najeriya daga 2010 zuwa 2015, sannan ta rike matsayin shugabar Kungiyar Kasashe Masu Arzikin Man Fetur ta Duniya (OPEC).


A cewar Shugaban Hukumar Yaki da Laifuffuka ta Birtaniya (NCA), Andy Kelly, “gurfanarwar da aka yi wa Diezani wata somin-tabi ce na wani zuzzurfan bincike na kasa da kasa da aka dade ana yi.”

Hukumar dai ta ce ana zargin Diezani da karbar akalla tsabar kudi har Fam din Ingila 100,000 da wasu motoci da hawa jirgin da ba na ’yan kasuwa ba, yin hutun kece raini ita da iyalanta da kuma yin amfani da gidaje masu yawa a birnin Landan.

An kuma zarge ta da nuku-nuku kan wasu kadarori masu tsada da ta mallaka da suka hada da kayan ɗaki da biyan kudin makarantar ‘ya’yanta da kuma wasu sarkoki da kayan ado.
(AMINIYA)

Monday, 10 April 2023

Burtaniya Ta Dakatar Da Daukar Ma'aikatan Lafiya Daga Najeriya

Gwamnatin Birtaniya ta dakatar da daukan ma’aikatan lafiya daga Najeriya.

Wannan dai na kunshe ne cikin sabuwar dokar daukan ma’aikatan ketare da Gwamnatin Birtaniyar ta yi wa kwaskwarima da ta wallafa a shafinta na Intanet.


Da wannan dai a yanzu Najeriya ta shiga sahun kasashen duniya da Kungiyar Lafiya ta Duniya WHO ta bayyana a matsayin masu bukatar gaggawa ta fuskar karancin ma’aikatan lafiya da za su jibinci lamarin kiwon lafiyarsu.

A watan Maris ne WHO ta wallafa sunayen kasashen duniya 55 da ke fama da karancin ma’aikatan lafiya ciki har da Najeriya.

Gwamnatin ta Birtaniya ta ce akwai bukatar Najeriya da sauran kasashen da lamarin ya shafa su mayar da hankali wajen bunkasa harkokin kiwon lafiyarsu musamman ta hanyar dakile daukar ma’aikatan lafiyarsu aiki da ake yi a ketare.

A ranar Alhamis ta makon jiya ce Majalisar Wakilai ta amince da kudirin da ke shirin tilasta wa likitoci share shekaru biyar a Najeriya kafin samun izinin zuwa kasashen waje aiki.

Wani dan Majalisar Wakilan na jam’iyyar APC daga Legas, Ganiyu Johnson, ne ya dauki nauyin kudirin da ke neman a yi wa Dokar Likitoci ta 2004 kwaskwarima.

Galibi ’yan majalisar da suka kada kuri’a baka sun amince da kudirin, sai dai wasunsu sun nemi a yi wa kudirin sakwa-sakwa ta yadda wadanda abin zai shafa za su samu zabin aiki a kasar ko tafiya ketare.

Wannan lamari dai wani sabon abu ne da ka iya kai wa ya zamo sabon rikici a tsakanin Gwamnatin Tarayyar da Kungiyar Likitoci NMA.

Ya zuwa yanzu, akalla likitoci dubu biyu ne ke barin kasar a shekara da sunan ci rani.

Haka kuma, kwarrarun likitocin Najeriya sun yi nisa a kasashen Turai da ’yan uwansu na Gabas ta Tsakiya, inda ke zaman sababbin matattarar likitocin da ke fadin ba dadi cikin kasar a halin yanzu.

To sai dai kuma bayan share tsawo na lokaci tana guna-guni a kuryar daki, tarrayar Najeriyar na neman mafita tare da wata dokar da ta tilasta daukacin likitoci na kasar share shekaru guda biyar suna aiki kafin samun izinin damar yin aiki can a kasashe na waje.

Dokar da ta tsallaka mataki na biyu na zauren majalisar, na da babban burin kawo karshen kaurar da likitoci ke yi zuwa ketare.

Duk da dimbin makarantun aikin likita, har ya zuwa yanzu yawan likitoci cikin kasar bai haura dubu 25 ba a Tarayyar Najeriyar da ke da mutane miliyan 200 da kadan.

Sabuwar dokar ta fara jawo takkadama, inda kungiyar likitoci ta kasar NMA ta ce, a kai ga kasuwa.

Kungiyar NMA dai ta ce, maimakon a dora wa kare laifin kura, kamata ya yi a kalli mai ya janyo maitar tun daga farko.

Kyautata tsarin aiki ko kuma kokari na murde wuyar ’yan cin rani dai, kusan kaso sittin cikin dari na likitoci na kasar a fadar kungiyar kananan likitoci na kasar na neman hanyar fita da nufin inganta rayuwa da makomar likitocin Najeriyar.

Ya zuwa yanzun, likita guda daya ne ke duban marasa lafiya dubu 30 a Kudancin kasar, a yayin da adadin ya kai dubu 45 a Arewacin kasar.
AMINIYA 

Thursday, 5 January 2023

Yarima Harry na Burtaniya ya zargi yayansa Yarima Williams da dukansa

Yarima Harry ya yi da'awar cewar yayansa Yarima William ya taɓa dukan sa, in ji jaridar Guardian, wadda ta ce ta ga wani ɓangare na littafin da yarima Harry ɗin ke rubutawa, mai taken 'Spare'.

Jaridar ta ruwaito cewa littafin ya ambato wani lokaci da aka samu sa-in-sa tsakanin ƴan'uwan biyu a kan matar Harry, Meghan.

Jaridar ta ce a cikin littafin Harry ya rubuta cewa "ya ci kwalata, ya tsinka sarƙar da ke wuyana, sannan ya bugani da ƙasa."

Sai dai Majiyarmu ba ta kai ga ganin littafin na 'Spare' ba.

Ba za a buga littafin ba sai ranar Talata ta sama, amma jaridar Guardian ta ce ta ga littafin a wani abu da ta kira " bugun kafin a wallafa".

Kawo yanzu fadar Buckingham ba ta ce komai ba, duk da cewa an tuntuɓe ta kan batun.bayar da rahoto kan lamarin, ba mu kira shi da faɗa ba, saboda Harry bai mayar da martani ba.

A cewar jaridar Guardian "Yarima Harry ya rubuta cewar ɗan uwansa ya nemi da ya rama bugun da ya yi masa, amma ya ƙi, sai dai daga baya Yarima William ya yi "nadama, ya kuma ba shi haƙuri".
Hotuna sun nuna yadda Yarima Harry ke sanya baƙar sarƙa, a taro irin na wasannin Invictus, da lokacin tafiya zuwa wata ƙasa shi da Meghan, kamar yadda suka yi a watan Satumbar 2019.

Har yanzu kamfanin wallafa littatafai na Penguin Random bai kai ga tabbatar da cewar ko wadancan bayanai da suka fita daga littafin, kan batun da Yarima Harry ya yi cewar yana da saɓani da ɗan uwansa, gaskiya ne ko kuwa akasin haka ba.

A wani fim na rayuwar Harry da Meghan na Netflix, Yarima Harry ya bayyana taron da ya halarta da ɗan uwansa, da mahaifinsa da yanzu ya zama sarki.

Yarima Harry ya bayyana taron farkon shekarar 2020, wanda marigayiya sarauniyar Ingila ta hallarta, da "abin kaɗuwa".

Yarima Harry ya ce "abin kaɗuwa ne, da na ji yayana na ihu da ɗaga murya gare ni, da mahaifina, yana faɗar abubuwa da babu gaskiya a cikinsu, kakata na zaune ta yi shiru tana jin abin da ke faruwa,".

Jaridar Guardian ta ce, Prince Harry ya bayar da cikakkun bayanai kan yadda zamansu ya kasance da Sarki Charles, a lokacin yana Yariman Wales, da Yarima William bayan jana'izar kakansa Yarima Phillip, a Afrelun 2021.

A cewar jaridar, Yarima Harry ya rubuta cewar, mahaifinsa ya shiga tsakaninsu shi da Yarima Williams, yana cewar "don Allah yara kar ku sa shekaruna na ƙarshe su kasance cikin ƙunci".

A wata hira da za a haska a ranar 8 ga watan Janairu, kafin sakin littafin, yariman ya ce: "Zan so na daidaita dangantakata da mahaifina da ɗan'uwana".

Ko da yake Yarima Harry ya shaida wa Tom Bradby na tashar ITV cewar, ba su nuna sha'awarsu ta son a daidaita ba," duk da cewar ba a fahimci taƙamaimai wa yake nufi ba.

Ko da aka tuntuɓi fadar Buckingham kan lamarin, ta ƙi cewa komai a kai.

A wani jawabi da kamfanin wallafa litattafai na Penguin Random ya yi a watan Octoban bara, ya ce "daga ƙarshe - wannan shi ne labarin Harry".

"Da irin tsagwaron gaskiyar da ke cikin littafin Spare, littafi ne da ke cike da bayanai, da tone-tone, da fadin ra'ayin kai, da darusan da ya koya kan mulki da soyyaya kan baƙin ciki.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...