Posts

Showing posts with the label Burtaniya

Birtaniya Ta Gurfanar Da Diezani A Gaban Kotu Kan Zargin Almundahana

Image
Kasar Birtaniya ta gurfanar da tsohuwar Ministar Man Fetur ta Najeriya, Diezani Alison-Madueke a gaban kotu kan zargin rashawa lokacin da take Minista. Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa ’yan sandar kasar sun ce sun maka ta a kotun ne saboda suna zargin ta karbi cin hanci a wasu kwangilolin man fetur da iskar gas. Diezani, mai shekara 63 a duniya, na daya daga cikin kusoshi a gwamnatin tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan. A zamanin mulkin tsohon Shugaban, Diezani ta rike mukamin Ministar Mai ta Najeriya daga 2010 zuwa 2015, sannan ta rike matsayin shugabar Kungiyar Kasashe Masu Arzikin Man Fetur ta Duniya (OPEC). A cewar Shugaban Hukumar Yaki da Laifuffuka ta Birtaniya (NCA), Andy Kelly, “gurfanarwar da aka yi wa Diezani wata somin-tabi ce na wani zuzzurfan bincike na kasa da kasa da aka dade ana yi.” Hukumar dai ta ce ana zargin Diezani da karbar akalla tsabar kudi har Fam din Ingila 100,000 da wasu motoci da hawa jirgin da ba na ’yan kasuwa ba,

Burtaniya Ta Dakatar Da Daukar Ma'aikatan Lafiya Daga Najeriya

Image
Gwamnatin Birtaniya ta dakatar da daukan ma’aikatan lafiya daga Najeriya. Wannan dai na kunshe ne cikin sabuwar dokar daukan ma’aikatan ketare da Gwamnatin Birtaniyar ta yi wa kwaskwarima da ta wallafa a shafinta na Intanet. Da wannan dai a yanzu Najeriya ta shiga sahun kasashen duniya da Kungiyar Lafiya ta Duniya WHO ta bayyana a matsayin masu bukatar gaggawa ta fuskar karancin ma’aikatan lafiya da za su jibinci lamarin kiwon lafiyarsu. A watan Maris ne WHO ta wallafa sunayen kasashen duniya 55 da ke fama da karancin ma’aikatan lafiya ciki har da Najeriya. Gwamnatin ta Birtaniya ta ce akwai bukatar Najeriya da sauran kasashen da lamarin ya shafa su mayar da hankali wajen bunkasa harkokin kiwon lafiyarsu musamman ta hanyar dakile daukar ma’aikatan lafiyarsu aiki da ake yi a ketare. A ranar Alhamis ta makon jiya ce Majalisar Wakilai ta amince da kudirin da ke shirin tilasta wa likitoci share shekaru biyar a Najeriya kafin samun izinin zuwa kasashen waje aiki. Wani dan Majali

Yarima Harry na Burtaniya ya zargi yayansa Yarima Williams da dukansa

Image
Yarima Harry ya yi da'awar cewar yayansa Yarima William ya taɓa dukan sa, in ji jaridar Guardian, wadda ta ce ta ga wani ɓangare na littafin da yarima Harry ɗin ke rubutawa, mai taken 'Spare'. Jaridar ta ruwaito cewa littafin ya ambato wani lokaci da aka samu sa-in-sa tsakanin ƴan'uwan biyu a kan matar Harry, Meghan. Jaridar ta ce a cikin littafin Harry ya rubuta cewa "ya ci kwalata, ya tsinka sarƙar da ke wuyana, sannan ya bugani da ƙasa." Sai dai Majiyarmu ba ta kai ga ganin littafin na 'Spare' ba. Ba za a buga littafin ba sai ranar Talata ta sama, amma jaridar Guardian ta ce ta ga littafin a wani abu da ta kira " bugun kafin a wallafa". Kawo yanzu fadar Buckingham ba ta ce komai ba, duk da cewa an tuntuɓe ta kan batun.bayar da rahoto kan lamarin, ba mu kira shi da faɗa ba, saboda Harry bai mayar da martani ba. A cewar jaridar Guardian "Yarima Harry ya rubuta cewar ɗan uwansa ya nemi da ya rama bugun da ya yi masa, amma ya