Search This Blog

Showing posts with label Hodar Iblis. Show all posts
Showing posts with label Hodar Iblis. Show all posts

Sunday, 14 May 2023

’Yan Kasuwa 2 Sun Yi Kashin Kunshi 193 Na Hodar Iblis A Hannun NDLEA

Wasu ’yan kasuwa biyu sun yi kashin kunshi 193 na Hodar Iblis bayan shafe kwanaki uku a hannun jami’an Hukumar Yaki da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA).

Bayanai sun ce an cafke ababen zargin biyu ne a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, a ranar 10 ga watan Mayu yayin shigowarsu Najeriya daga kasar Uganda.

Haaland ya zama dan kwallon da babu kamarsa a Firimiyar Ingila a bana
Angola ta zarce Najeriya a hako danyen man fetur —OPEC
Mai Magana da Yawun NDLEA, Femi Babafemi ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Lahadin.

Mista Babafemi ya ce an dade ana neman mutanen biyu ruwa a jallo wadanda ake zargi ba su da wata sana’a face safarar miyagun kwayoyi.

Ya bayyana cewa bayan shafe kwanaki a hannun hukumar, daya daga cikinsu ya yi kashin kunshi 100 na Hodar Iblis wanda nauyinta ya kai kilo 2.137, yayin da abokin tafiyarsa ya yi kashin kunshi 93 na hodar mai nauyin kilo 1.986.

Kazalika, jami’an NDLEA sun kai samame wata mashayar miyagun kwayoyi a titin Bama da ke Sabon Gari da kuma Filin Wasa na Sani Abacha da ke birnin Kano, inda suka cafke ababen zargi 160 dauke da miyagun kwayoyi daban daban-daban.

Haka kuma, hukumar ta cafke wasu mutum biyu a titin Kano zuwa Maiduguri da tarin miyagun kwayoyi da suka hada da kwayoyi 5,000 na tramadol.

Wannan na zuwa ne a yayin da jami’an hukumar suka cafke wasu ababen zargi 25 a yankunan Tora Bora, Gwarinpa, Karmo, Kasuwar Garko, Bwari da sansanin ’yan gudun hijira na Kucigoro da ke Abuja.




Sunday, 1 January 2023

Mun Kama Bako Da Kullin Hodar Iblis 105 Daga Brazil —NDLEA



Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta kama kullin hodar iblis 105 a cikin kayan wani wanda ya dawo daga kasar Brazil a Babban Jirgin Sama na Murtala Mohammed da ke Legas.

Daraktan yada labarai na hukumar, Femi Babafemi, ya sanar ranar Lahadi a Abuja cewa sun kama wanda ake zargin ne ranar Kirsimeti.

Ya ce wanda ake zargin na daga cikin fasinjojin da suka dawo daga birnin Sao Paulo na kasar Brazil.

A cewarsa, bayanan sirrin da suka samu sun taimaka wajen kama wanda ake zargin a filin jirgin.

Da aka tsananta bincike a kansa karo na biyu, sai aka gano hodar iblis din da yake dauke da ita, in ji jami’in.

Shugaban NDLEA na Kasa, Birgediya-Janar Buba Marwa (Murabus), ya sha nanata cewa ba za su raga wa masu fataucin miyagun kwayoyi ba ko’ina suke a fadin kasa.

(AMINIYA)

(NAN)

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...