Search This Blog

Showing posts with label Lambar Yabo. Show all posts
Showing posts with label Lambar Yabo. Show all posts

Thursday, 7 September 2023

Kungiyar Kannywood Ta Bawa Kwamishinan Kudi Na NAHCON Lambar Yabo

Da yake jawabi, jagoran tawagar Alhaji Ahmed Kaka ya taya hukumar murnar kammala aikin Hajjin 2023 cikin nasara duk da kalubalen da ake fuskanta.

A sanarwar da Shafi'i Sani Muhammad na sashen yada labarai da Dab'i na Hukumar NAHCON ya sanyawa hannu, Shugaban kungiyar ya yi kira da a hada kai a tsakanin bangarorin guda biyu musamman ta fannin wayar da kan alhazai da tsawaita amfani da kafafen sada zumunta na zamani.

Kungiyar ta baiwa Alhaji Nura Hassan Yakasai, Kwamishinan kudi lambar yabo ta taimakon jin kai bisa gudunmawar da ya bayar wajen bayar da muhimmin taimako ga marasa galihu a cikin al’umma.

Alhaji Yakasai wanda ya bayyana jin dadinsa ga dandalin ya tabbatar musu da shirye-shiryen Hukumar na yin bincike da hada kai da kungiyar nan gaba.


Tunda farko da yake nasa jawabin, Shugaban Hukumar NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan ya yi kira ga ‘yan wasan kwaikwayon Najeriya da su ci gaba da amfani da kafar sadarwar su wajen wayar da kan ‘yan Nijeriya musamman Alhazai ta hanyar fasaharsu.
Ya bayyana haka ne a yau a lokacin da kungiyar Kannywood Action Forum karkashin jagorancin Alhaji Ahmed Kaka ta kai ziyarar ban girma ga hukumar NAHCON a  Abuja.

Shugaban ya bayyana imaninsa cewa tare da dimbin masu sauraronsu musamman a Arewacin Najeriya, ayyukansu ko labaransu za su taimaka matuka wajen nuna kyakykyawan kimar kasar da kuma taimakawa wajen kawo canji ga al’umma.


Wednesday, 18 January 2023

Mun Kashe $1bn Wajen Kwato Yankunan Da ’Yan Ta’adda Suka Mamaye – Buhari


Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya ce Najeriya ta kashe sama da Dala biliyan daya wajen sayen makaman da ta yi amfani da su wajen yaki da ’yan ta’adda tun 2015.

Buhari ya bayyana haka ne ranar Talata sa’ilin da yake jawabi a wajen Babban Taron Zaman Lafiya na Afirka na 2023, da ya gudana a birnin Nouakchott, Jamhuriyar Musulunci ta Murtaniya.


Shugaban wanda aka karrama da lambar yabo ta “Karfafa Zaman Lafiya a Afirka” a Abu Dhabi, ya ce akwai bukatar a rungumi dabi’ar karrama juna da mutuntawa a makarantu, musamman kuma a tsakanin matasa.

Haka nan, ya yi kira ga shugabanni da su bai wa rayuwar matasa muhimmanci ta hanyar horar da su sana’o’in hannu domin maganin zaman kashe wando.

Cikin sanarwar da ya fitar ta hannun mai magana da yawunsa, Femi Adesina, Buhari ya ce dole a ba da himma wajen hana ta’ammali da kananan bindigogi da sauran makamai a cikin al’umma.

Kana ya bukaci yayin taron kasashen Afirka na gaba, a dauki matakin lalubo hanyar magance matsalolin da ke ci gaba da yi wa kasar Libiya tarnaki wanda hakan ya sa kasar ta zama dandalin ta’ammali da makamai da mayakan ketare.

“Ta’addanci da fashin daji da sauran

Ya kara da cewa kafewar Tafkin Chadi ta haifar wa al’ummar yankin rasa hanyoyinsu na samun masarufin rayuwa wanda hakan ya yi sanadiyyar jefa dimbin matasan yankin cikin kungiyoyin ‘yan ta’adda.


A karshe, Buhari ya yi godiya ga Majalisar Zaman Lafiya ta Abu Dhabi karkashin jagorancin Shaykh Abdallah Bin Bayyah, bisa karrama shi da ta yi da lambar yabon.



Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...