Search This Blog

Showing posts with label Majalisa. Show all posts
Showing posts with label Majalisa. Show all posts

Thursday, 2 November 2023

Majalisa Ta Yi Fatali Da Bukatar Tinubu Ta Kashe Biliyan 5 Wajen Sayen Jirgin Ruwa

Majalisar Wakilai a ranar Alhamis ta yi fatali da bukatar Shugaban Kasa Bola Tinubu ta kashe Naira biliyan 5 daga cikin kwarya-kwaryar kasafin kudin tiriliyan 2.17 wajen sayen jirgin ruwa.

A maimakon haka, majalisar ta bukaci a mayar da kudin wajen kara yawan kuɗin da aka ware domin ba dalibai rancen, wanda a baya aka ware wa biliyan 10.

‘Barayin’ da suka je fashi sun ɓige da satar tukwanen miya da abinci a Kalaba
Majalisa ta amince da kwarya-kwaryar kasafin kudin Tinubu na tiriliyan 2.17
Aminiya ta rawaito cewa matakin ’yan majalisar ba zai rasa nasaba da koke-koken da ’yan Najeriya suka rika yi ba tun bayan bullar labarin, inda suka ce ya zo a daidai lokacin da ’yan kasa ke korafin kuncin rayuwa.

Shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, Abubakar Kabir (APC, Kano) ne ya bayyana hakan lokacin da yake yi wa manema labarai jawabi jim kadan da kammala amincewa da kasafin a Abuja.

Ya ce daukar matakin ya zama wajibi la’akari da kudin da aka ware wa daliban a cikin kasafin ya yi kadan.

Abubakar ya kuma ce kwamitin ya kason da aka ware wa Ma’aikatar Tsaro daga Naira biliyan 476 zuwa 546 sakamakon ƙaruwar kalubalen tsaro.

Shugaban kwamitin ya kuma ce sun duba tare da amincewa da batun kara mafi ƙarancin albashin ma’aikata domin mika shi ga bangaren zartarwa.

Sai dai ya ce za su tabbatar suna sanya idanu ga bangaren zartarwa domin ganin sun yi abin da ya dace.

Amma daga bisani Fadar Shugaban Kasa ta ce jirgin ruwa ba na amfanin Tinubu ba ne, na Rundunar Sojin Ruwan Najeriya ne
(AMINIYA)

Friday, 6 January 2023

Jihohin Najeriya na neman Majalisar wakilai ta sa su cikin harkar samar da wuta

Kwamitin majalisar wakilan Najeriya da ke kula da harkokin wutar lantarki ya yi zama don jin ra'ayin jama'a, game da wani garambawul da majalisar ke shirin yi ga dokar lantarki domin bai wa jihohi damar shiga harkar samar da wuta.


Kwamitin ya ɗauki matakin ne bayan da jihohi suka nemi a basu damar shiga harkar a matakai daban-daban, da suka haɗa da samarwa da kuma rarrabawa.


Mahukunta a Najeriya dai sun sha nuna rashin gamsuwa da yadda kamfanonin wutar lantarkin suke gudanar da harkokinsu.


Honourable Magaji Ɗa'u Aliyu, shugaban kwamitin ya shaida wa BBC cewa "akwai kamfanin da ke ruwa da tsaki wajen tafiyar da harkokin wutar lantarki a ƙasar, sai dai ya ce jihohi a yanzu sun nemi a basu dama "su je su yi nasu".


"Mun saurare su, kuma sun kawo mana kundin da suka yi aiki a kai, za mu duba shi sannan kuma za mu faɗa musu halin da ake ciki a kai."

A cewarsa, gaba ɗaya jihohin Najeriya sun sa hannu a takardar da aka miƙa musu "har sun aiko da wakilai daga jihohi guda shida."shida.

Ban da gwamnatocin jihohi, ƙungiyoyi da wasu ɗaiɗaikun jama'a su ma sun bayyana nasu ra'ayin, kuma mafi yawa na nuna goyon baya ga yunƙurin da majalisar ke yi na gyaran fuska ga dokar wutar lantarkin.

Ita ma gwamnatin Najeriya a nata ɓangaren ta ce ta yi na'am da maganar garambawul ɗin sosai sakamakon rashin gamsuwar da ta yi da takun kamfanonin da aka damƙa wa samar da wutar lantarkin a halin da ake ciki.

Minista a ma'aikatar wutar lantarki a Najeriya, Mista Goddy Jedy Agba, ya bayyana cewa yin gyaran na da muhimmanci ga al'ummar ƙasar.

"Muna son gyaran, kowa na son wuta a Najeriya, idan an yi aikin sai mu samu ci gaba."

Ya ce akwai matakai na samar da wutar lantarki - samarwa da rarrabawa kuma a halin da ake ciki, gwamnati kawai tana samar da wutar ne kawai.

"A wannan shekara, za mu cire hannu daga samarwa, zai zama kowa zai taka rawa"

Kwamitin wutar lantarkin dai ya ce zai miƙa bayanan da ya tattara ga zauren majalisar wakilai, kuma a can ne za a yi tankaɗe da rairaya gabanin yanke shawara a kan abin yi.

Batun inganta wutar lantarki daɗaɗɗiyar magana ce a Najeriya, da aka yi yunƙuri daban-daban tun gabanin komawar ƙasar ga dimokraɗiyya, aka kuma ci gaba da kwan-gaba-kwan-baya har zuwa yau.

Kodayake za a iya cewa wutar da ake samarwa ta ƙaru a tsukin nan, amma kuma a ɓangare guda, ƴan ƙasar na kukan cewa ta yi ɗan karen tsada.

Tuesday, 3 January 2023

Yau sabuwar majalisar Amurka za ta yi zamanta na farko

A yau Talata sabuwar majalisar dokokin Amurka za ta fara aiki inda dan Republican Kevin McCarthy zai nemi zama shugaban majalisar wakilai.

Bayan zaben rabin wa’adi da a aka yi a watan Nuwamba, ‘yan Republican sun karbe ragamar shugabancin majalisar wakilai amma da dan kankanin rinjaye.

Majalisar dokokin Amurkar a wannan ta rabu gida biyu, inda ‘yan Democrat suka ci gaba da rike shugabancin majalisar dattawa yayin da ‘yan Republican suke karbe majalisar wakilai.

Wani abu da zai fi jan hankali a yau shi ne yadda ‘yan Republican za su zabi shugaban majalisar ta wakilai.

McCarthy na fatan ganin ya gaji Nancy Pelosi ‘yar Democrat amma kuma yana fuskantar kalubalen rashin samun goyon baya - har daga abokansa.

Wannan shi ne karon farko cikin shekaru 100 da dan takarar neman shugabancin majalisar wakilai ya gaza samun goyon baya daga wasu ‘yan jam’iyyarsa.

Tsohon Shugaban Amurka Donald Trump na goyon bayan McCarthy.

Dan majalisar wakilai Andy Riggs na jihar Arizona da Steve Scalia mai wakiltar Louisiana na daga cikin ‘yan Republican din da suke adawa da McCarthy.

Bayanai sun yi nuni da cewa daukacin ‘yan Democrat ba za su goyi bayan McCarthy ba, abin da ke nufin dole sai dai ya mayar da hankalinsa kan kuri’un ‘yan Republican.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...