Search This Blog

Showing posts with label Asusun Gwamnatin Tarayya. Show all posts
Showing posts with label Asusun Gwamnatin Tarayya. Show all posts

Friday, 6 January 2023

An haramta cire tsabar kudi daga asusun Gwamnati

Hukumar da ke sanya ido kan hada-hadar kudade a Najeriya (NFIU) ta haramta cire tsabar kudi daga asusun Gwamnatin Tarayya da jihohi da kuma kananan hukumomi daga ranar 1 ga watan Maris, 2023.

NFIU ta ce daga ranar, laifi ne a biyan ma’aikatan gwamnati alawus-alawus din tafiyar aiki a cikin gida ko zuwa kasashen waje da tsabar kudi.

An gano gawar mutum 16 a hatsarin jirgi a Kebbi
’Yan sanda sun cafke ’yan daba 63 a taron Tinubu a Kano
Babban Daraktan hukumar, Modibbo Tukur, ne ya bayyana haka a Abuja ranar alhamis, inda ya ce karin wasu sabbin tsare-tsaren na tafe.

Ya ce za a fara amfani da sabbin tsare-tsaren ne bayan fara aikinsa dokar Babban Bankin Najeriya (CBN) na takaita cirar tsabar kudi ga daidaikun mutane da kamfanoni a Najeriya.


Da yake karin haske kan dokokin, Modibbo ya ce hakan yayi daidai da sashi na 3(1)a-s, da sashi na 23(2) na kundin hukumar.

A baya dai bisa dalilai daban-daban, ma’aikatun gwamnati da hukumomi, na fitar da kudade daga bankuna don yin mu’amalar kasuwanci a hukumance da ba a iya ganowa cikin sauki, maimakon ta hanyar musayar bankuna.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...