Posts

Showing posts with the label Al-Nassr

Al Nassr za ta mutunta hukuncin dakatarwar wasanni 2 kan Ronaldo

Image
  Kungiyar kwallon kafa ta Al Nassr a Saudi Arabia ta tabbatar da shirin mutunta hukuncin hukumar kwallon kafar Ingila kan sabon dan wasan da kungiyar ta saya Cristiano Ronaldo game da haramcin wasanni biyu da ke kansa Wani jigo a Al Nassr ya shaidawa AFP yau juma’a cewa tauraron na Portugal mai shekaru 38 ba zai taka leda a wasanni biyu da kungiyar za ta doka nan gaba ba, domin mutunta hukuncin.   Tun a watan Nuwamba ne dai, hukumar FA ta dakatar da Ronaldo a wasanni biyu saboda samunsa da laifin jifan wani magoyin bayan Everton da wayar salula lokacin da ya ke shirin daukar hotonsa bayan rashin nasarar Manchester United hannun Everton a Goodison Park. Har zuwa yanzu dai Al Nassr ba ta yiwa Ronaldo rijista ba, kasancewar kungiyar ta zarta adadin ‘yan wasa 8 sa hukumar kwallon kafar Saudiya ta sahale mata saye daga ketare duk kaka. Zuwa yanzu dai Al Nassr ta sayi ‘yan wasan da yawansu ya kai 9 daga ketare ciki har da Ronaldo da ta sayo kan yuro miliyan 200 bayan dan wasan gaban na Port

Kungiyoyi da dama sun so daukata amma na yi wa Al-Nassr alkawari - Ronaldo

Image
Cristiano Ronaldo ya ce kungiyoyin kwallon kafa da dama a sassan duniya sun nuna sha’awar daukar sa amma ya yanke shawarar sanya wa Al-Nassr hannu. A lokacin da Al-Nassr ta gabatar da shi a matsayin dan wasanta a gaban dubban magoya bayan kungiyar a ranar Talata, Ronaldo ya bayyana cewa kungiyoyi a nahiyar Turai da Brazil Amurka da Australia da Portugal sun nemi su dauke shi amma ya zabi zuwa Saudiyya. Jaridar Aminiya ta rawaito Ronaldo na cewa “Kamar yadda na fada a baya wannan dama ce a gare ni ba wai a harkar kwallon kafa ba, dama ce da zan sauya tunanin matasa masu tasowa. “Kungiyoyi da dama daga Nahiyar Turai da Brazil da Amurka da Australia da ma Portugal son so dauka ta amma na yi wannan kungiya alkawari. “Na san abin da nake so da wanda ba na so, kuma wannan babban kalubale ne a gare ni na zuwa wannan kasa, ba don komai ba sai don na kara samun ilimi. “Ina son sabon yanayi, kasa don cimma wani buri na daban tare sa Al-Nassr, wannan shi ne dalilin da ya sa na rungumi