Posts

Showing posts with the label BBC Hausa a

Muhawarawar 'yan takarar gwamna ta BBC : Kungiyar Global Group Ta Taya Gwamna Ganduje Murnar bisa Kwazon Gawuna

Image
Wata kungiya ta duniya da ta kware wajen tantance muhawarar siyasar ‘yan takara a fadin duniya , Dandalin tantance muhawarar siyasa (PODAF) ta taya gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano murnar kwazon da mataimakin gwamnan jihar kuma dan takarar gwamna na jihar, Nasiru Yusuf Gawuna ya yi a wajen muhawarar yan takarar gwamna da Sashen Hausa na Gidan Rediyon Birtaniya (BBC) ya shirya a Makarantar koyar da harkokin Kasuwancin Aliko Dangote da ke Jami’ar Bayero, Kano, ranar Asabar. A cikin wata wasika da aka aika wa gwamnan kuma mai dauke da sa hannun babban jami’in kungiyar na Najeriya, Mista Johnson Craig, ya bayyana cewa, “Mun gamsu matuka da yadda mataimakin ku, wanda kuma dan takarar gwamna ne na jam’iyyar APC ya yi a lokacin da aka kammala muhawarar zaben gwamna da sashen Hausa na BBC ya shirya." Cikin sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwaman, Malam Abba ya fitar, ta ce Wasikar a wani bangare na cewa, “Kungiyarmu ta ga ya zama dole mu taya mai girma gwa