Search This Blog
Monday, 11 December 2023
Labari Da Dumiduminsa: 'Yan Majlisar Jahar Rivers 27 Masu Biyayya Ga Wike Sun Bar PDP Zuwa Jam'iyyar APC
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Monday, 2 January 2023
Kotun Senegal ta daure 'yan majalisa saboda dukan mace
Kotu a Senegal ta yanke hukuncin daurin watanni 6 a kan ‘yan majalisar dokokin kasar su biyu na bangaren 'yan adawa, saboda samun su da laifin dukar abokiyar aikinsu daga bangaren masu rinjaye.
A ranar 1 ga watan Disambar da ya gabata ne dan majalisar dokoki Massata Samb ya yi dirar mikiya a kan wata ‘yar majalisar mai suna Amy Ndiaye, bisa zargin furta kalaman batanci a kan Moustapha Sy, shugaban wata jam’iyyar siyasa da ke cikin gungun ‘yan adawa sannan kuma shehin malamin addinin musulunci da ake mutuntawa a kasar.
Wasu hotuna da ake rika yadawa sun nuna yadda Massata Samb ya lafta wa Amy Sy mari a cikin zauren majaliar ‘yayin da abokinsa dan majalisa Mamadou Niang ya sa kafa ya noshi matar a ciki bainar jama’a.
Bayan faruwar wannan lamari, an kwantar da ‘yar majalisa Amy Sy a asibiti bayan da bayanai suka tabbatar da cewa tana dauke da juna biyu a lokacin faruwar lamarin, to sai dai a lokacin da yake yanke hukunci, alkali ya yi watsi da zargin yunkurin kisa kamar dai yadda masu shigar da kara suka bukata.
Ko baya ga hukuncin dauri, hakazalika kotun ta bukaci mutanen biyu su biya tarar cfa jika dari a matsayin diyya saboda dukar da suka yi wa ‘yar majalisar wadda ta fito daga jam’iyyar shugaba Macky Sall.
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa
Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct
The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...
-
Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya ce Bankuna za su ci gaba da karbar tsoffin takardun kudi na Naira ko da baya...
-
Matar hamshakin dan kasuwa na Kano, Alhaji Aminu Alasan Dantata, Hajiya Rabi ta rasu Jaridar SOLACEBASE ta rawaito cewa, Hajiya ...
-
Zababben Gwamnan Jihar Kano Ya Sanar Da Kwamitin Karbar Mulki …… Dr. Baffa Bichi, Abdullahi Musa ya nada a matsayin Shugaba da Sakatare Baya...
