Search This Blog

Showing posts with label Hudu Ari. Show all posts
Showing posts with label Hudu Ari. Show all posts

Saturday, 6 May 2023

Zaben Adamawa: An Ba Da Belin Kwamishina Hudu

 


’Yan sanda sun bayar da belin Kwamishinan Zabe na Jihar Adamawa da aka dakatar, Hudu Yunusa-Ari, bayan da ya yi kwana uku a tsare a hannunsu.

’Yan sanda sun cafke shi ne kan wata sanarwa mai cike da rudani da ya yi  cewa Sanata Aisha Dahiru Binani ta lashe zaben gwamnan jihar Adamawa, alhali ba a kammala karbar sakamakon karashen zaben ba.

Tun a lokacin INEC ta soke sanarwar, sannan ta bukaci ya gabatar da kansa a hedikwatarta da ke Abuja, amma maimakon ya je, sai ya yi layar zana.

Daga bisani hukumar ta rubuta Shugaban ’Yan Sandan Najeriya wasikar neman ya binciki kwamishinan zaben, kan yamutsa hazon da ya yi.

Amma wata wasika da ya aike wa shugaban ’yan sanda, Hudu ya ce ya yi sanarwar ne a bisa doka, saboda dalilan tsaro.

A ranar Talala ’yan sanda suka sanar cewa sun kama Hudu, wanda ya ce ba ya nadamar sanarwar da ya ya yi cewa Binani ta ci zabe.

Amma kakakin rundunar ’yan sandan Najeriya, Muyiwa Adejobi, ya sanar a ranar Juma’a cewa rundunar ta bayar da belin kwamishinan zaben.

Muyiwa ya cen an umarci Hudu ya rika zuwa hedikwatar rundunar a ranakun aiki domin ci gaba da binciken da ake gudarwa.

AMINIYA

Monday, 24 April 2023

‘Yan sanda sun fara farautar shugaban INEC na Adamawa


Babban Sufeton 'yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba ya umurci wata tawagar 'yan sanda ta yi aiki tare da hukumar zaben Najeriya INEC wajen bincike da kuma gurfanar da shugaban hukumar zabe na jihar Adamawa da aka dakatar Hudu Yunusa Ari.

A wata sanarwar da rundunar ta fitar wacce kakakinta Olumuyiwa Adejobi ya sanya wa hannu, babban sufeton ya ce 'yan sanda za su tabbatar sun yi dukkan mai yiwuwa domin gano dalilin da ya sa Hudu aikata abun da ya yi.

Ana tsaka da tattara sakamakon zaɓen gwamna na jihar Adamawa da aka ƙarasa ne sai kwatsam Hudu wanda shi ne kwamishinan zaɓe na jihar, ya ayyana Sanata Aishatu Binani ta APC a matsayin wadda ta lashe zaɓen.

IGP Usman ya ce a shirye su ke su tabbatar an yi hukunci da ya dace kan dukkan wadanda aka samu da hannu a lamarin da ya faru a Adamawa domin martaba dokokin dimokradiya.

Sanarwar ta tabbatar wa 'yan Najeriya da kuma kasashen duniya cewa 'yan sanda za su binciki ayyana Aishatu Binani ta APC da Hudun ya yi tare sauran masu hannu a lamarin domin gurfanar da su a gaban kotu.

Tuni dai Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da matakin hukumar zaɓen ƙasar na dakatar da kwamishinan na INEC a Adamawa ya zuwa lokacin da za a kammala bincike.

Buhari ya umarci gudanar da bincike da gurfanar da Hudu Ari gaban shari'a, matuƙar an same shi da laifi.

A baya dai hukumar zaben Najeriya ta INEC ta ce ba ta san inda Hudu Ari ya shiga ba tun lokacin da ta dakatar da shi.

BBC

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...