Search This Blog

Showing posts with label Jami'ar Kogi. Show all posts
Showing posts with label Jami'ar Kogi. Show all posts

Thursday, 16 May 2024

Karin Dalibai 7 Na Jami'ar Kogi Sun Shaki Iskar 'Yanci

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kogi ta ce an kuɓutar da ƙarin wasu ɗalibai bakwai da aka sace a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Confluence da ke yankin Osara a jihar


Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Williams Aya, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

Aminiya ta ruwaito kamar yadda hukumar ‘yan sandan ta tabbatar cewa an sace ɗalibai 24 a jami’ar kuma zuwa yanzu an ceto 21 daga ciki.

Ya ce Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nijeriya, IGP Kayode Egbetokun, ya tura ƙwararru domin ci gaba da aikin ceto ragowar ɗaliban da ke hannun masu garkuwa da su.


“An tura sashen tsaro na rundunar ‘yan sanda na sama, wanda ya ƙunshi jami’an rundunar masu amfani da jirgi masu saukar ungulu da aka horar da su kan binciken ta sama da jami’an sa ido da kuma sashen leƙen asiri na fasaha (TIU) don ci gaba da aikin ceton da kuma kai farmaki kan masu aikata laifuka a jihar.


“Ƙwararru jami’an tsaro tare da haɗin gwiwa ne suka kai ga ceto ƙarin mutane bakwai (7) da aka sace wanda ya kawo adadin zuwa 21.

“Muna nan akan bakarmu wajen ci gaba da duk mai yiwuwa domin tabbatar da cewa an kuɓutar da dukkan ɗaliban cikin aminci tare da gurfanar da waɗanda suka aikata laifin domin a hukunta su,” in ji shi.


Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar Kogi da ma al’ummar jami’ar sun gamsu da aikin ceton da ake yi kawo yanzu.


Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Benthrad Onuoha, ya yabawa Sufeta Janar ɗin bisa goyon baya kan aikin da suke gudanarwa.
(AMINIYA)


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...