Posts

Showing posts with the label LP

Yanzu-Yanzu : Dan Takarar Gwamnan Kano Na Jam'iyyar LP, Bashir I Bashir Ya Koma APC

Image
Dan takarar gwamna na jam’iyyar Labour Party, LP, a jihar Kano, Bashir Bashir, ya fice daga jam’iyyarsa zuwa jam’iyyar All Progressives Congress, APC. A ranar 21 ga watan Janairu, dan takarar gwamnan ya kaurace wa taron gangamin jam’iyyar a Kano tare da shugaban kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, Mohammed Zarewa; kodinetan yakin neman zaben Peter Obi na jiha, Balarabe Wakili da; dan kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, Idris Dambazau. Wata majiya da ke kusa da dan takarar ta tabbatar da sauya shekar Mista Bashir da wasu jiga-jigan jam’iyyar LP zuwa APC a ranar Lahadin da ta gabata, inda ta ce babban dalilin da ya sa suka sauya sheka shi ne na ware manyan masu ruwa da tsaki a Arewa wajen yanke shawara da kuma rashin samun cikakkiyar alkibla kan maslahar Arewacin Najeriya. .

Hukumar DSS ta kama tsohon Shugaban Kungiyar Yakin Neman Zaben dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar LP, Doyin Okupe

Image
Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta kama tsohon Shugaban Kungiyar Yakin Neman Zaben dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar LP, Doyin Okupe. A cewar Tolu Babaleye, lauyan Okupe, an kama dan siyasar ne a filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Ikeja a Jihar Legas, a lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa Landan. Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja, ta samu Okupe, mai bai wa tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan shawara kan Harkokin Jama’a, da laifin karkatar da kudaden makamai daga Ofishin mai bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaro. Mai shari’a Ijeoma Ojukwu ta bayyana cewa, masu tuhuma sun gabatar da karar satar kudi a kan Okupe wanda aka ci shi tarar Naira miliyan 13. Jaridar Aminiya ta rawaito cewa, A shekarar 2019, Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arziki Zangon Kasa, ta tuhumi Okupe da laifuka 59 ciki har da wadanda suka shafi karkatar da kudi har Naira miliyan 240 daga hannun Sambo Dasuki. An gurfanar tare da shi tare da wasu kamfanoni biyu – Value T