Search This Blog

Friday, 13 January 2023

Hari Kan NSCDC: Kar Ku Raga Wa ’Yan Bindiga —Buhari Ga Sojoji


 Shugaba Buhari ya yi Allah wadai da kisan jami’an Sibil Difens bakwai da wasu ’yan bindiga suka yi a Kaduna.

Cikin wata sanarwa da kakakinsa Garba Shehu ya fitar ranar Alhamis, Buharin ya bayyana takaicinsa da kisan jajirtattun jami’an da ya ce sun sadaukar da rayuwarsu ga Najeriya.

“Jami’an NSCDC din da suka sadaukar da rayuwarsu wajen tsare kasarmu ba karamin jihadi suka yi ba a bakin aikinsu.

“Ina jajanta wa iyalai da ’yan uwa da abikan arzikinsu. Ina rokon Ubangiji Ya ba su ikon jure wannan rashi”, in ji Buhari.

Daga nan ne kuma shugaban ya umarci rundunar sojojin Najeriya da su kamo ’yan bindigar su yi maganinsu.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...