Posts

Showing posts with the label Ganduje Mazaba

APC Ta Kano Ta yi Tir Da Dakatarwar Da Aka Yi Wa Ganduje, Ta Kuma Sanyawa Shugabannin Mazabar Takunkumi

Image
Kwamitin ayyuka na jam’iyyar APC reshen jihar Kano, ya kakabawa jiga-jigan mazabar Ganduje takunkumi bisa dakatar da shugaban jam’iyyar na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje daga jam’iyyar. Shugaban jam’iyyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas, wanda ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano a ranar Litinin din da ta gabata, ya ce an dakatar da shugabannin unguwar Ganduje na tsawon watanni shidda saboda wasu ayyukan da suka saba wa jam’iyya. Abbas ya ce kwamitin ayyuka na jihar ya yi Allah-wadai da matakin dakatarwar sakamakon amincewa da matakin kwamitin karamar hukumar Dawakin Tofa na jam’iyyar. “Muna da shaidar ganawar da jami’an gwamnatin jihar suka yi da wadanda suka dakatar da shugaban kasa na kasa, kuma kwamitin gudanarwa na jihar ya amince da sanya musu takunkumi na tsawon watanni shida, kuma an dakatar da su,” inji shi. A ranar Litinin din da ta gabata ne shugabannin unguwar Ganduje a karamar hukumar Dawakin Tofa suka sanar da dakatar da Dakta Ganduje bisa zargin c