Posts

Showing posts with the label Kwamishina

Nan Ba Da Jimawa Ba Matsalar Ruwa Za Ta Zama Tarihi A Kano - Kwamishina

Image
Gwamnatin jihar Kano ta ce tana bakin kokarinta wajen ganin ta shawo kan matsalar karancin ruwan sha a birnin Kano da kewaye. Kwamishinan albarkatun ruwa na jihar Dr Ali Haruna Makoda ne ya bayyana hakan a wata hira da manema labarai a Kano ranar Laraba. “Muna aiki tukuru domin ganin mun gyara matsalar karancin ruwan sha a babban birnin jihar da kewaye, kuma nan ba da jimawa ba za a kawo karshen matsalar,” inji Makoda. Ya dora alhakin kalubalen a kan cikakken kayan aiki, musamman a cibiyar kula da ruwa ta Tamburawa da ke samar da ruwa ga mafi yawan sassan birnin Kano. Ya ce tsananin zafin da ake fuskanta a yankin shi ma ya jawo matsalar karancin ruwan, yayin da mutane ke amfani da ruwa mai yawa don jure yanayin. A cewarsa, gwamnatin jihar ta gaji lalacewar sha’anin ruwa daga gwamnatin da ta shude wanda ba ta ba da kulawar da ya kamata ba wajen samar da ruwan sha. A lokacin gwamnatin da ta shude, kwamishinan ya ce kashi 20 cikin 100 na bukatun ruwan jihar ne kawai ake samar

Gwamnatin Kano Ta Musanta Cin Zarafin Yara A Gidan Marayu

Image
  Gwamnatin Jihar Kano ta yi watsi da rahoton zargin cin zarafin yara da wasu jami’anta suka yi a gidan marayu da ke Nassarawa a jihar. Kwamishinar Harkokin Mata da Ci Gaban Al’umma ta jihar, Dakta Zahra’u Muhammad Umar, ta yi watsi da rahoton yayin da ta zanta da manema labarai a ranar  “Wasu masu yin barna ne suka hada labarin don bata sunan gwamnatin jihar nan. “Amma abin da ta faru shi ne ba mu da hurumin ci gaba da zama da kuma kulawa da yaran da suka haura shekara 18 a gidan marayu. Doka ma ba ta ba mu wannan damar ba. “An bukaci wasu mutum biyu, Ladidi da Saudat da su bar gidan marayun tun da yanzu sun zama manya.” Jaridar Aminiya ta rawaito cewa kwamishinar Ta bayyana cewa matan biyu, wadda daya daga ciki bazawara ce, dayar kuma na da aure har da ’ya’ya uku, sun ki barin gidan sannan sun shiga yi wa kwamishinar bita da kulli da sauran ma’aikatan don bata musu suna. “Sun shiga gidan rediyon sun yi kazafin cewar ana cin zarafin yara, ana kai su wurare daban-daban ba bisa ka’ida b