Search This Blog

Showing posts with label Danbatta. Show all posts
Showing posts with label Danbatta. Show all posts

Saturday, 4 March 2023

Hajjin Bana: Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Yi Kira Ga Maniyyata Aikin Hajin Bana, Da Su Cika Kudinsu Ya Kai Miliyan Biyu Da Dubu Dari Diya


Sakaaren zartarwa na hukumar, Ambasada Muhammad Abba Danbatta ne, yayi wannan kiran a ranar Asabar cikin wata sanarwa da ya bayar.

Danbatta yace tun a ranar 28 ga watan da ya gabata ne wa’adin da hukumar kula da aikin hajji ta kasa (NAHCON) ta bayar ga hukumomin kula da jin dadin alhazai na jahohi, na cika kudaden adadin kujerun da aka basu ya kare, inda suka nemi alfarmar kara wa’adi domin bawa maniyyatan dama

“Bayan sanya hannu kan yarjejeniya ta gudanar da aikin Hajjin 2023 ta umarci jahohi da su kai a kalla daga miliyan daya da dubu dari biyar zuwa sama”

Sakataren zartarwar wanda ya bayyana cewa tun a kwanakin baya, bayan da suka dawo daga kasa Indonesiya wajen taron masu ruwa da tsaki kan harkokin aikin Hajji na kasa da kasa, yace a lokacin hukumomi sun fito da sababbin dokoki wanda aka umarci hukumomin alhazai na johohi su fadawa maniyyatansu dasu cika kudinsu ya kai naira miliyan biyu da dubu dari biyar kafin a ayyana kudin kujerar

“Wannan ne ya sa muke kira ga maniyyata wadanda suka biya ko aka biya musu, dasu cika kudinsu ya kai naira miliyan biyu da dubu dari biyar kafin a tantance abun da za a biya”

 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...