Search This Blog

Showing posts with label Boko Haram. Show all posts
Showing posts with label Boko Haram. Show all posts

Monday, 20 May 2024

An ceto mutane 386 bayan shekaru 10 a hannun Boko Haram



Sojoji sun ceto fararen hula 386, akasarinsu mata da kakanan yara, daga Dajin Sambisa, bayan Boko Haram ta sace su kimanin shekaru goma da suka gabata.

Mai rikon mukamin Babban Kwamandan Birget Din Sojin Kasa Na 7, Birgedia AGL Haruna, ne ya bayyana haka ranar Lahadin yayin da yake zantawa da manema labarai a gefen dajin da ke karamar hukumar Konduga ta jihar Borno sakamakon nasarar kammala wani aiki na kwanaki 10 da aka yi wa lakabi da “Operation Desert Sanity 111”.

A cewarsa, an kai farmakin ne da nufin kawar da duk wani burbushin Boko Haram da sauran ’yan ta’adda da ke dajin gami da bayar da dama ga masu son mika wuya su yi hakan.


Janar Haruna ya bayyana fatansa na cewa karin ’yan ta’adda za su mika wuya, inda ya bayyana yadda suke ci gaba da mika wuya ga sojoji.


“Kokarin da muke yi shi ne mu tabbatar da cewa mun kawar da ragowar ’yan ta’adda a Sambisa, tare da bai wa masu son mika kansu damar yin hakan.


“Da wannan aiki, muna sa ran da yawa daga cikinsu za su mika wuya kamar yadda suka fara.


“Mun kuma ceto wasu fararen hula guda 386 a ranar 17 ga Mayu, 2024; kuma na tabbata adadin zai karu,” inji Haruna.


Janar Haruna ya yaba wa sojojin bisa kwazon da suka nuna, ya kuma bukace su da su ci gaba da gudanar da ayyukansu.


Monday, 15 May 2023

Dan jarida, Ndace, ya wallafa littatafai uku kan yadda Buratai yai nasarar yaƙi da Boko Haram/ISWAP

Jibrin Baba Ndace, tsohon wakilin jaridar Blueprint a ɓangaren tsaro, ya bayyana cewa ya rubuta littattafai uku ne a kan yaƙi da ta'addanci duba da yadda tsohon Shugaban Hafsoshin Sojojin Ƙasa, COAS, Laftanar Janar Tukur Buratai (mai ritaya), duba da irin jajircewar sa wajen yakin.

An ƙaddamar da littattafan, masu taken  “Walking the War Front with Lt. Gen. TY Buratai,” “Duty Call Under Buratai’s Command” da kuma  “The Lonely Grave and Other Poems" a ranar Asabar da ta gabata a dakin taro na Shehu Musa Yar’adua da ke Abuja.

Da ya ke magana game da dalilin da ya sa ya fara aikin wallafa litattafan, wanda ya kwashe shekaru biyar yana rubutawa, Ndace, tsohon babban sakataren yada labarai, CPS, ga Gwamna Abubakar Sani Bello na jihar Neja, ya lura cewa ya sami kwarin gwiwa da bukatar rubuta littattafan ne na yakin da ake yi da masu tada kayar baya a matsayin sa na ganau ba jiyau ba.

“Wadannan littattafan sun samu goyon baya da gudunmawa daga tsoffin sojoji da suka taka rawa a fagen yaƙi. Sojojin da su ka sadaukar da rayukansu don bauta wa ƙasar mu da jajircewar da suka nuna da kuma abubuwan da suka faru na ban tsoro.

“Daga cikin sojoji da masu yi wa kasa hidima, Laftanar Janar TY Buratai ya mamaye babban bangare na labarin.

“Lt. Janar TY Buratai Janar ne na sojan Najeriya mai ritaya, tsohon babban hafsan sojin kasa, wanda aka nada a shekarar 2015 kuma ya yi ritaya a watan Janairun 2021,” in ji mawallafin.

Da ya ke sanya albarka a wajen taron, Zaɓaɓɓen Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya ce littattafan da ke bayyana yakin da ake yi da mayakan Boko Haram/ISWAP a yankin Arewa maso Gabas an rubuta su ne musamman domin taimakawa wajen ganin irin ta’addancin da su ke yi a kan yan kasa.

Ya kara da cewa littattafan sun kuma nuna irin kwazon Sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro, Civilian JTF su ke yi wajen yaƙi da ƴan Boko Haram da ISWAP a karkashin jagorancin Hafsan Sojoji na 20, Laftanar Janar TY Buratai.

Shettima, wanda Sen. Ibrahim Hassan Hadejia ya wakilta, ya yaba wa Ndace, mawallafin littattafan wajen kwazo da hazakar da ya nuna a matsayin sa na ganau a yaki da ƴan ta'adda.

Ya bayyana littattafan na Ndace ba kawai a matsayin 'tatsuniyoyi kawai ba, sai dai cewa fitattun ayyukan basira ne na gaskiya da gaskiya.

Shettima ya lura cewa masu karatun littattafan na Ndace da aka buga a cikin su za su sami labarin gaskiya na yadda sojojin Najeriya su ka kasance a sahun gaba wajen kare martabar kasar daga kungiyar Boko Haram da kungiyar Islamic State of West Africa, ISWAP.

Sauran manyan baki da su ka tofa albarkacin bakinsu, musamman Ministan Tsaro, Manjo - Janar Bashir Salihi Magashi (mai ritaya), sun yabawa Ndace bisa gagarumin aikin da ya yi na fito da yadda yaƙi da Boko Haram da nasarorin da aka samu.

Tuesday, 25 April 2023

’Yan Matan Chibok’ 2 Sun Gudo Daga Hannun Boko Haram


 Karin mutum biyu daga cikin daliban Makarantar Sakandaren ’Yan Mata da ke Chibok a Jihar Borno sun gudo daga hannun mayakan Boko Haram da suka sace su shekaru tara da suka gabata.

Majiyoyin tsaro da mazauna Jihar Borno sun shaida wa wakilinmu cewa matan su biyu sun samu tserewa a dalilin tsananta luguden wuta da sojoji suke yi a kan sansanonin kungiyar da ke Dajin Sambisa

Wata majiyar tsaro ta ce daliban da suka gudo su ne Hauwa Mutah da kuma Esther Markus.

Ta bayyana cewa, “Daya daga cikinsu ’yar kauyen Chibok ce, dayar kuma ’yar kauyen Dzilang ce.”

Mako biyu da suka gabata, rundubar soji ta Operation Hadinkai da ke yaki da kungiyar, ta bayyana cewa akwai saura mutum 98 daga cikin Daliban Chibok a hannun kungiyar.

Kwamandan Sashen Lelen Asiri na rundunar, Kanar Obinna Ezuipke ya ce, “Daga cikin Daliban Chibok 276 da aka sace, 57 sun tsere a 2014, an sako 107 a 2018.

Friday, 6 January 2023

Ana shirin mayar da tubabbun mayaƙan Boko Haram 613 cikin al'umma

Hukumomi a Najeriya sun kammala shirin miƙa wasu mayaƙan Boko Haram fiye da 600 da suka tuba ga gwamnatocin jihohinsu domin shigar da su cikin sauran al`umma.

Hedikwatar tsaron Najeriyar ta bayyana cewa an ɗauki wannan matakin ne bayan an shigar da su cikin wani shirin gyara hali.

 BBC Hausa ta rawaito Hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Lucky Irabor ya bayyana cewa an kammala shirin miƙa mayakan Boko Haram ɗin da suka tuba su 613, bayan an gyara musu hali.

Ya yi bayanin ne a wajen wani taron masu hannu ko ruwa da tsaki a ƙarƙashin tsarin nan na ba da damar miƙa wuya ko tuba ga mayaƙan Boko Haram, wato Operation Safe Corridor.

Ya ce za a mika su ne ga jihohinsu na asali domin shigar da su cikin al`umma, kuma a halin da ake ciki ana gab da kammala aikin sauya musu tunani da zare musu tsattsaurar akida.

 A cewar Hafsan hafsoshin, tubabbun mayakan Boko Haram ɗin na bukatar kulawa sosai a wannan gaɓa ta gyara hali da sake shiga cikin jama`a, don haka sai jihohin sun tsaya sosai a kan su.

Batun gyara hali aikin ne jawur, saboda ko a nasu matakin sai da suka haɗa da kwararru daga fannoni daban-daban, da ma'aikatu da hukumomin gwamnati masu yawa, da kuma taimakon kungiyoyin agaji na kasa da kasa.

Ya ce za yi nasarar shigar da tsoffin mayakan cikin al'umma idan jihohi suka yi tsari mai kyau, tare da haɗa gwiwa da sarakunan gargajiya wajen sa-ido a kan tubabbun yayin da suke sajewa a cikin al'umma.

Janar Irabor ya ce idan aka zo sallama ko yaye tsoffin ƴan Boko Haram din, za a ba su guzurin kayan abinci da kayan zaman gida da kuma kayan aiki irin sana'ar da suka koya don fuskantar gangariyar rayuwa.

Game da yakin da ake yi da kungiyar Boko Haram kuwa, Hafsan hafsoshin ya ce askarawan gwamnati na samuN nasara a kan su, kuma da dama sai mika wuya suke yi sakamakon mamayar dajin Sambisa da zaratan sojojin suka yi da fatattakar su da ake yi inda ta kai ga fiye da mayakan Boko Haram da iyalansu 80,000 sun mika wuya.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...