Posts

Showing posts with the label Boko Haram

An ceto mutane 386 bayan shekaru 10 a hannun Boko Haram

Image
Sojoji sun ceto fararen hula 386, akasarinsu mata da kakanan yara, daga Dajin Sambisa, bayan Boko Haram ta sace su kimanin shekaru goma da suka gabata. Mai rikon mukamin Babban Kwamandan Birget Din Sojin Kasa Na 7, Birgedia AGL Haruna, ne ya bayyana haka ranar Lahadin yayin da yake zantawa da manema labarai a gefen dajin da ke karamar hukumar Konduga ta jihar Borno sakamakon nasarar kammala wani aiki na kwanaki 10 da aka yi wa lakabi da “Operation Desert Sanity 111”. A cewarsa, an kai farmakin ne da nufin kawar da duk wani burbushin Boko Haram da sauran ’yan ta’adda da ke dajin gami da bayar da dama ga masu son mika wuya su yi hakan. Janar Haruna ya bayyana fatansa na cewa karin ’yan ta’adda za su mika wuya, inda ya bayyana yadda suke ci gaba da mika wuya ga sojoji. “Kokarin da muke yi shi ne mu tabbatar da cewa mun kawar da ragowar ’yan ta’adda a Sambisa, tare da bai wa masu son mika kansu damar yin hakan. “Da wannan aiki, muna sa ran da yawa daga cikinsu za su mika wuya

Dan jarida, Ndace, ya wallafa littatafai uku kan yadda Buratai yai nasarar yaƙi da Boko Haram/ISWAP

Image
Jibrin Baba Ndace, tsohon wakilin jaridar Blueprint a É“angaren tsaro, ya bayyana cewa ya rubuta littattafai uku ne a kan yaÆ™i da ta'addanci duba da yadda tsohon Shugaban Hafsoshin Sojojin Ƙasa, COAS, Laftanar Janar Tukur Buratai (mai ritaya), duba da irin jajircewar sa wajen yakin. An Æ™addamar da littattafan, masu taken  “Walking the War Front with Lt. Gen. TY Buratai,” “Duty Call Under Buratai’s Command” da kuma  “The Lonely Grave and Other Poems" a ranar Asabar da ta gabata a dakin taro na Shehu Musa Yar’adua da ke Abuja. Da ya ke magana game da dalilin da ya sa ya fara aikin wallafa litattafan, wanda ya kwashe shekaru biyar yana rubutawa, Ndace, tsohon babban sakataren yada labarai, CPS, ga Gwamna Abubakar Sani Bello na jihar Neja, ya lura cewa ya sami kwarin gwiwa da bukatar rubuta littattafan ne na yakin da ake yi da masu tada kayar baya a matsayin sa na ganau ba jiyau ba. “Wadannan littattafan sun samu goyon baya da gudunmawa daga tsoffin sojoji da suka taka

’Yan Matan Chibok’ 2 Sun Gudo Daga Hannun Boko Haram

Image
  Karin mutum biyu daga cikin daliban Makarantar Sakandaren ’Yan Mata da ke Chibok a Jihar Borno sun gudo daga hannun mayakan Boko Haram da suka sace su shekaru tara da suka gabata. Majiyoyin tsaro da mazauna Jihar Borno sun shaida wa wakilinmu cewa matan su biyu sun samu tserewa a dalilin tsananta luguden wuta da sojoji suke yi a kan sansanonin kungiyar da ke Dajin Sambisa Wata majiyar tsaro ta ce daliban da suka gudo su ne Hauwa Mutah da kuma Esther Markus. Ta bayyana cewa, “Daya daga cikinsu ’yar kauyen Chibok ce, dayar kuma ’yar kauyen Dzilang ce.” Kawo yanzu daliban makarantar 96 ne suka rage a hannun kungiyar Boko Haram da ta sace su tun a watan Afrilun shekarar 2014. Mako biyu da suka gabata, rundubar soji ta Operation Hadinkai da ke yaki da kungiyar, ta bayyana cewa akwai saura mutum 98 daga cikin Daliban Chibok a hannun kungiyar. Kwamandan Sashen Lelen Asiri na rundunar, Kanar Obinna Ezuipke ya ce, “Daga cikin Daliban Chibok 276 da aka sace, 57 sun tsere a 2014, an sako 107 a

Ana shirin mayar da tubabbun mayaƙan Boko Haram 613 cikin al'umma

Image
Hukumomi a Najeriya sun kammala shirin miÆ™a wasu mayaÆ™an Boko Haram fiye da 600 da suka tuba ga gwamnatocin jihohinsu domin shigar da su cikin sauran al`umma. Hedikwatar tsaron Najeriyar ta bayyana cewa an É—auki wannan matakin ne bayan an shigar da su cikin wani shirin gyara hali.  BBC Hausa ta rawaito Hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Lucky Irabor ya bayyana cewa an kammala shirin miÆ™a mayakan Boko Haram É—in da suka tuba su 613, bayan an gyara musu hali. Ya yi bayanin ne a wajen wani taron masu hannu ko ruwa da tsaki a Æ™arÆ™ashin tsarin nan na ba da damar miÆ™a wuya ko tuba ga mayaÆ™an Boko Haram, wato Operation Safe Corridor. Ya ce za a mika su ne ga jihohinsu na asali domin shigar da su cikin al`umma, kuma a halin da ake ciki ana gab da kammala aikin sauya musu tunani da zare musu tsattsaurar akida.  A cewar Hafsan hafsoshin, tubabbun mayakan Boko Haram É—in na bukatar kulawa sosai a wannan gaÉ“a ta gyara hali da sake shiga cikin jama`a, don haka sai jihohin sun tsaya sosai