Search This Blog

Showing posts with label Abba Gida-gida. Show all posts
Showing posts with label Abba Gida-gida. Show all posts

Friday, 26 May 2023

Gabanin Rantsuwa: Zababben Gwamnan Kano, Abba Gida Gida Ya Bayyana Kadarorinsa

Gabanin kaddamar da taron a ranar Litinin, zababben gwamnan jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, (wanda aka fi sani da Abba Gida Gida) ya bayyana kaddarorin sa da kuma bashin da ake bin sa a cikin fom din da ya cike  ya mika a ranar Juma’a ga ofishin hukumar da'ar ma'aikata dake Kano 

SOLACEBASE  ta rahoto cewa  Abba wanda ya samu tarba daga Daraktar hukumar ta jihar Kano Hajia Hadiza Larai Ibrahim, ya bayyana cewa kwazonsa na bayyana kadarorinsa nuni ne na gaskiya da rikon amana da zai zama ginshikin gwamnati mai zuwa a jihar Kano.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sunusi Bature Dawakin Tofa babban sakataren yada labarai na zababben gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya fitar a ranar Juma’a.

Ya ce: "A yau, na cika hakkin da kundin tsarin mulki ya dora min na bayyana kadarorina kafin na shiga Ofis, ranar 29 ga Mayu."

''Zababben Gwamna,  ya shaida wa mata cewa aikin gwamnati kira ne; hidima ce ga bil’adama kuma a shirye nake a koyaushe in yi hidima bayan samun amincewar mutanen jihar Kano, in ji sanarwar.

''Bugu da kari, Engr. Abba ya bayyana cewa a halin yanzu haka komai ya fito fili don tafiyar maido da ci gaba mai dorewa a dukkan bangarori, inda duk wani Kobo na asusun gwamnati da aka kashe ba kawai zai zama ta hanyar rashin gaskiya ba, har ma a jihar Kano karkashin kulawar sa.

‘’Ya ba da tabbacin cewa dukkan jami’an gwamnati da suka hada da masu rike da mukaman siyasa da za su yi aiki a gwamnatinsa za a ba su izinin bin tsarin bayyana kadarorin kamar yadda doka ta tanada.

Wednesday, 29 March 2023

Yanzu-Yanzu: Nasiru Gawuna Ya Taya Abba Gida-gida Murnar Lashe zaɓen Gwamnan Kano

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Kuma wanda ya yiwa jam’iyyar APC takarar gwamnan jihar kano a jam’iyyar APC Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya ce ya karɓi Kaddarar faɗuwa zaɓe tare da taya Abba Kabiru Yusuf Murnar lashe zaɓen gwamnan Kano.

Nasiru Gawuna ya bayyana hakan ne cikin wani sakon murya da yayi bayani na tsawon mintuna biyu, wanda Sakataren yada labaran sa Hassan Musa Fagge ya aikowa kadaura24.


” Mun tsammaci Hukumar Zabe INEC zata duba koken da mukai mata na samun kura-kurai a sakamakon zaben da ya gudana, amma a yau 29 ga watan maris ta sake tabbatar da matsayar ta ta hanyar mikawa Abba Kabiru Yusuf Shaidar lashe zabe , don haka mun dauki wannan a matsayin kaddara”. Inji Gawuna


 
Yace dama ya fada a baya cewa zai karɓi Kaddara idan ya fadi zaben don haka yayi kira ga magoya bayan sa da dukkanin al’ummar jihar kano da zu baiwa sabon zaɓaɓɓen gwamnan hadin kai don ya gudanar da mulkin sa cikin kwanciyar hankali da lumana.

 
Mataimakin Gwamnan ya kuma yi addu’ar Allah ya kamawa Sabon zababben gwamnan, sannan yayin addu’ar Allah ya bashi ikon yiwa al’ummar jihar kano adalci a Shugabanci sa.
KADAURA24 


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...