Posts

Showing posts with the label Masu Bayar da shawara na musamman

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Sake Yin Wasu Karin Nade-Nade A Gwamnatinsa

Image
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin wasu mutane a matsayin masu bashi shawara na musamman a bangarori daban-daban  A sanarwar da babban sakataren yada labaran gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ta ce wadanda aka nada din sun hada da : 1. Kanal Abubakar Usman Garin Malam mai ritaya a matsayin mai bawa Gwamna shawara na musamman Kan kula da harkokin iftila'i.  2. Malam Usamatu Salga, mai bada shawara na musamman Kan al'amuran addini 3. Abduljabbar Muhammad Umar , mai bawa Gwamna shawara Kan harkokin zuba Jari da Kuma kulla alaka da bangarorin da ba na gwamnati 4. Aminu Abba Ibrahim, mai bawa Gwamna shawara kan albarkatun kasa 5. Injiniya Nura Hussain, mai bawa Gwamna shawara kan harkokin ciniki 6. Jamilu Abbas, mai bawa Gwamna shawara na musamman Kan kungiyoyin tsumi da tanadi 7. Muhammad Jamu Yusuf, mai bawa Gwamna shawara na musamman kan dangantaka da Kasashen Waje da na waje  8. Balarabe Ibrahim Gaya, mai bawa Gwamna shawara na musamman Kan shirye