Posts

Showing posts with the label Shinkafa

Kwastam ta kama tirelar shinkafa ‘yar-waje takwas da aka shigar Nijeriya

Image
Hukumar fasa-ƙwauri ta Nijeriya, Kwastam ta ce ta kama tirela takwas maƙare da shinkafa ƴar-waje a kan iyakokin ƙasar da ke yankin Kudu maso Yamma. A wani taron manema labarai da Shugaban Kwastam na riƙo Bashir Adewale Adeniyi ya yi a Legas wanda ya ce mai matuƙar muhimmanci ne ga tattalin arzikin ƙasar, ya ce jami’an hukumar sun kama shinkafar buhu 7,029 ne a lokuta da wurare daban-daban a shiyyar Kudu maso Yammacin. Mr Adeniyi ya ce an samu wannan nasara ce bayan ƙaddamar da wasu jerin ayyuka da hukumar ta yi don ceto fannin noma na ƙasar da ya zama babban makamin da gwamnatin tarayya ke riƙe da shi don inganta samar da abinci. “Kamar yadda aka sani fannin noma, wanda shi ne ƙashin bayan tattali arzikin Nijeriya, ya zama muhimmin abun da gwamnatin tarayya ta mayar da hankali a kai don samar da isasshen abinci ga ƴan ƙasar da kuma inganta tattalin arziki. “Ana gudanar da wannan samame da jami’anmu ke yi ne don abu biyu ne; karya gwiwar ƴan kasuwar da ke son su dinga hada-h