Posts

Showing posts with the label Hukunci

Kotu Ta Sauya Hukunci Kan Dakatar Da Ganduje A Matsayin Shugaban APC Na Kasa

Image
Babbar kotun jihar Kano mai lamba hudu karkashin mai shari’a Usman Na’abba, wadda tun da farko ta yi   umarnin dakatar da Abdullahi Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasa, ta yi watsi da wannan umurnin na korar dakatar da shi A wani umarni na baya-bayan nan da kotun ta bayar kan tsohon gwamnan jihar Kano, wanda yanzu shi ne shugaban jam’iyyar APC mai mulki ta kasa, an haramtawa tsohon gwamnan jihar Kano gabatar da kansa a matsayin Shugaban jam'iyyar na kasa bayan wani Haladu Gwanjo da Laminu Sani Barguma da ke ikirarin cewa shi ne shugaba da sakataren jam’iyyar na APC a mazabar Ganduje a karamar hukumar Dawakin Tofa ta jihar, suka bayar da umarnin dakatar da Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar. Sai dai kuma a wani yanayi na daban, alkalin babbar kotun jihar, Mai shari’a Usman Na’Abba, ya ce, a lokacin da ya yi watsi da umarnin da ya bayar a baya, ya ce da ya karanta takardar daukaka kara tare da takardar goyon bayan sakin layi na 27 da kuma rubutaccen adire

Kotun Koli Ta Jingine Yanke Hukunci Kan Zaben Gwamnan Nasarawa

Image
Kotun Koli da ke zamanta a Abuja ta jingine yanke hukuncin kan shari’ar Zaben Gwamnan Jihar Nasarawa, zuwa wata rana da za ta sanar nan gaba. A zamanta na yau Talata, Kotun Kolin ta saurari muhawarori daga lauyoyin bangarorin PDP da APC, kan takaddamar kujerar gwamnan jihar, tsakanin gwamna mai ci, Abdullahi Sule na jami’iyar APC da David Emmanuel Ombugadu na jami’iyar PDP. Tun farko dai, David Emmanuel Ombugadu na jam’iyyar PDP ya garzaya gaban Kotun Kolin bayan Kotun Daukaka Kara ta ayyana Abdullahi Sule a matsayin wanda ya lashe zaben. Wannan na dai na zuwa ne saÉ“anin hukuncin da Kotun Sauraron Kararrakin zabe ta yanke inda ta ayyana David Emmanuel Ombugadu a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar. Aminiya ta ruwaito cewa, a watan Nuwambar bara ne Kotun Daukaka Karar ta bayyana cewa kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar ta yi kuskure wajen soke nasarar Abdullahi Sule na APC a zaben Gwamnan Nasarawa da aka gudanar ranar 18 ga Maris, 2023. Ana iya tuna cewa,