Posts

Showing posts with the label Yarjejeniya

Hajj2023 : Kamfanonin Jiragen Sama na Najeriya, Sun Sanya Hannu kan Yarjejeniyar Jigilar Alhazai

Image
Hukumar alhazai ta kasa NAHCON da kuma kamfanin jiragen saman Najeriya hudu sun amince da jigilar maniyyata zuwa aikin hajjin 2023 daga karshe sun sanya hannu kan yarjejeniyar jigilar alhazai ta 2023 tsakanin bangarorin biyu.  A sanarwar da Mataimakin Daraktan yada labarai na hukumar NAHCON, Mousa Ubandawaki ya fitar, Taron wanda ya gudana a dakin taro na gidan Hajji a ranar Talata, ya samu halartar shuwagabannin kungiyoyin hudu. A nasa jawabin, Shugaban Hukumar NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, ya yabawa kishin kasa da kamfanonin jiragen sama suka sadaukar domin tunkarar kalubalen da rikicin kasar Sudan ke fuskanta.  “Ba mu manta da kalubalen da rufe sararin samaniyar kasar Sudan ya haifar ga aikin Hajjin ku ba; duk da haka, ina so in yi kira ga lamirinku da kishin Æ™asa da ku da kada ku Æ™ara dora wa mahajjata Æ™arin kuÉ—i ko canje-canje”. A jawabansu daban daban, Manajan Daraktan Kamfanin  Jirgin Aero, Kaftin Ado Sanusi ya ce jiragen ba su damu da halin da Alhazan da su