Posts

Showing posts with the label Dillalan Man Fetur

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Yi Kira Ga Masu Gidajen Man Fetur Dasu Dasu Siyar Da Mai A Tsohon Farashi

Image
Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusif ya bukaci ‘yan kasuwar man fetur da su dawo da farashin man fetur na baya domin rage wahalhalun da jama’a ke fuskanta a halin yanzu. A sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, tace Gwamnan ya ce yana sane da cewa har yanzu ‘yan kasuwar na da tsohon man fetur da ya kamata a sayar da shi a tsohon farashi. Domin rage wahalhalun da ‘yan jihar ke fama da su, ya kamata ‘yan kasuwa su yi hakuri su sake bude duk gidajen mai da kayayyakin da ake da su a hannun jari don sayarwa a kan tsohon farashi. “A matsayina na Gwamna, na ji takaicin ganin yadda Al’ummarmu na Kano ke shan wahala sakamakon hawan man fetur da bai dace ba, kuma dole ne a kawo karshen lamarin nan take.” Inji Gwamnan. Kano a cewar Gwamna Abba Kabir, ita ce cibiyar kasuwanci a yankin arewacin kasar da kuma wasu kasashe a yammacin Afirka, kuma al'ummarta masu tarin yawa na ci gaba da samun kyakkyawan yanayin kasuwanci.

Dillalan Man Fetur Sun Lashe Amansu Kan Shiga Yajin Aiki

Image
’ Yan sa’o’i bayan umartar mambobinta su rufe ilahirin gidajen man fetur a Najeriya, Kungiyar Dillalan Man Fetur ta Kasa (IPMAN) ta bukaci a bude gidajen a ci gaba da sayarwa. Aminiya ta rawaito yadda a ranar Talata kungiyar ta bukaci a rufe ilahirin gidajen man da ke kasar nan take sannan a fara yajin aiki, kamar yadda wata sanarwa da Shugaban kungiyar na kasa, Mohammed Kuluwa, ya fitar ranar Talata. IPMAN ta ce, “Sakamakon mawuyacin halin da muka tsinci kanmu a ciki wajen samo man da kuma sayar da shi da tsada, da kuma yadda hukumomi ke tilasta mana sayar da shi a kan farashin da muke faduwa. “Muna umartar ilahirin mambobinmu da su dakatar da sayar da mai, sannan su dakatar da biyan kudin duk wani man da suka riga suke kokarin sarowa daga yanzu har sai abin da hali ya yi.” To sai dai ’yan sa’o’i bayan waccan sanarwar, IPMAN ta yi mi’ara koma baya. “Bayan tattaunawa da hukumomi masu ruwa da tsaki, muna umartar gidajen mai da su bude su ci gaba da sayarwa, yayin da uwar kun