Posts

Showing posts with the label Hukumar Da'ar ma'aikata

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Umarci Dukkanin Kwamishinonin Da Zai Nada, Su Bayyana Kadarorinsu

Image
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya umurci dukkan wadanda aka nada na kwamishinoni 19 su bi ka’idojin da’ar ma'aikata A sanarwar da babban sakataren Yada labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, tace, da wannan sanarwar, ana sa ran wadanda aka zaba za su bayyana kadarorinsu a cikin mafi kyawun lokaci kafin a fara tantance su a majalisar dokokin jihar a ranar Alhamis 22 ga watan Yuni, 2023 da karfe 10 na safe a harabar majalisar dokokin jihar. Gwamnan ya sha alwashin cewa babu wani kwamishina da za a rantsar da shi a matsayin memba na majalisar zartaswa ta jihar ba tare da cike fom din bayyana kadarorinsa daga Ofishin hukumar kula da da'ar ma'aikata ba. "Duk sauran masu rike da mukaman siyasa a karkashin wannan gwamnati su ma za su bi umarnin da aka ba su." Gwamna Abba Kabir Yusuf na fatan jaddada aniyarsa ga mutanen jihar Kano nagari cewa gaskiya da rikon amana ya kasance tushen tsarin gwamnatinsa wanda za a yi amfani da shi wa

Gabanin Rantsuwa: Zababben Gwamnan Kano, Abba Gida Gida Ya Bayyana Kadarorinsa

Image
Gabanin kaddamar da taron a ranar Litinin, zababben gwamnan jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, (wanda aka fi sani da Abba Gida Gida) ya bayyana kaddarorin sa da kuma bashin da ake bin sa a cikin fom din da ya cike  ya mika a ranar Juma’a ga ofishin hukumar da'ar ma'aikata dake Kano  SOLACEBASE  ta rahoto cewa  Abba wanda ya samu tarba daga Daraktar hukumar ta jihar Kano Hajia Hadiza Larai Ibrahim, ya bayyana cewa kwazonsa na bayyana kadarorinsa nuni ne na gaskiya da rikon amana da zai zama ginshikin gwamnati mai zuwa a jihar Kano. Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sunusi Bature Dawakin Tofa babban sakataren yada labarai na zababben gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya fitar a ranar Juma’a. Ya ce: "A yau, na cika hakkin da kundin tsarin mulki ya dora min na bayyana kadarorina kafin na shiga Ofis, ranar 29 ga Mayu." ''Zababben Gwamna,  ya shaida wa mata cewa aikin gwamnati kira ne; hidima ce ga bil’adama kuma a shirye nake a koyaushe in