Posts

Showing posts with the label Katsina

Shugaban Majalisar Dokoki Ta Katsina Ya Raba Tallafin Naira Miliyan 35

Image
Kakakin Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, Nasir Yahaya, ya bayar da tallafin Naira Million Talatin da Huɗu da Dubu Ɗari Tara da Hamsin. (34,950,000) ga Mutum Dubu Ukku (3000) a filin wasan Ƙwallon Kafa dake Daura Hadimin tsohon Shugaban Najeriya, Buhari Sallau, ya rawaito a shafinsa na Facebook cewa, an bayar da Tallafin ga Marayu, Limamai, Zawarawa, Masu Ƙananan Sana'oi, Exco, Mata, Matasa, Students, yan Media, Dagattai, Mabuƙata, yan siyasa, Ƙungiyar Teloli, Ƙungiyar Masu Shayi da Masu chajin waya, da sauran su. Inda ko wanne daga cikinsu zai amfana da Tallafin, Naira Dubu Goma (10,000) Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda PhD, yayi Jin-Jina gami da fatan Alkhairi ga Kakakin Majalissar akan wannan abin Alkhairi da yayi, sannan yayi roƙo gami da Jan hankali ga wanda suka amfana da wannan Tallafin da suyi amfani dashi ta hanyar daya dace, domin su bunƙasa Kasuwar su.  Haka kuma Mataimakin Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar, Alh. Bala Abu Musawa, ya taya mutanen D

2023:Za Mu Sama Wa Katsina N10bn Daga Hasken Rana A Shekara —NNPP

Image
Dan takarar Gwamnan Katsina a Jam’iyyar NNPP, Nura Khalil, yi alkawarin tara kudaden shiga Naira biliyan 10 daga hasken rana a duk shekara a jihar. Injiniya Nura Khalil ya ce kudaden shigar N10bn da jihar za ta rika samu daga bangaren hasken rana zai sa ba sai ta jira daga Asusun Tarayya ba. A gaggauta kammala masana’atar tiransfomar Najeriya —Buhari A jawabinsa a taron fara yakin neman zabensa a Karamar Hukumar Mashi, ya ce, “Na fara da Mashi ne saboda da ita da Daurawa ta Jihar Jigawa da Kankiya bisa ga binciken da muka yi sun fi samar da hasken rana da za ta samar da lantarki ba sai an jira daga wani wuri ba. “Za mu yi amfani da wannan hasken wutar lantarkin don sama wa jihar kudaden shigar da akalla za a samu bilyan N100 a shekara. “Kudaden za mu yi amfani da su wajen gudanar da ayyukan gwamnati ba sai mun jira na Gwamnatin Tarayya ba.” Ya kara da cewa idan ya ci zaben da ke tafe a watan Maris, “Muna da shirin kafa banki mallakar gwamnatin jiha wanda zai iya bayar da d