Search This Blog

Showing posts with label Katsina. Show all posts
Showing posts with label Katsina. Show all posts

Saturday, 1 February 2025

Athletics Champ: How Maryam Saad, Female Artist Thrilled Gombe Crowd inside Pantami Stadium

Katsina State based female artist Maryam Sa'ad was a delight to watch as she thrilled the crowed at the official opening ceremony of 2025 of Gombe Inter Secondary Schools Athletics which held on Tuesday at the Pantami Stadium, Gombe State.

The Katsina born music artist lived up to expectations as her songs and artistic display on stage saw spectators dancing to frenzy. 

The 23 year-old graduate of Katsina State College of Education performed for 20 minutes and her songs received a good applouse and was commended by Director General of the competition, Hon Ahmed Gara Gombe and other guests who had to stepped down from the VIP stand to join in the dancing spree.

Speaking after her brilliant performance, female artist said she started her music career at Seven in Katsina and she had performed in various states and composed different songs for politicians and other dignitaries in the Northern part of Nigeria.

She also expressed her gratitude to Hon. Gara Gombe for inviting her to perform at a huge event of this magnitude and extended her appreciation to fans for the love showed during her performance.

"I am happy that the good people of Gombe accepted my songs and I thank Honourable Gara Gombe for giving me the opportunity to perform in Patanmi Stadium where more than 2,000 children were in attendance,"she said. 

Saar said she would continue to remain focused and ensure that she uses her songs to put smile on the faces of youths in Northern part of Nigeria.

Speaking in the same vein, Manager of popular artist, Abubakar Bature said he was not suprised with the performance of Saad saying that she has natural talents in music when she started seven years ago in Katsina.

"I came across her in 2017 and I observed that Saad is gifted in music.Since I became her manager,she has been improving tremendously.

"I am happy that she was at her best at the official opening ceremony of Gombe Inter Secondary Schools Athletics championship and principal cup football competition.She has not reached her pinnacle of music career yet I am still planning to get a job for her in other states especially in Lagos and outside the country,"he said

Wednesday, 20 December 2023

Shugaban Majalisar Dokoki Ta Katsina Ya Raba Tallafin Naira Miliyan 35

Kakakin Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, Nasir Yahaya, ya bayar da tallafin Naira Million Talatin da Huɗu da Dubu Ɗari Tara da Hamsin. (34,950,000) ga Mutum Dubu Ukku (3000) a filin wasan Ƙwallon Kafa dake Daura

Hadimin tsohon Shugaban Najeriya, Buhari Sallau, ya rawaito a shafinsa na Facebook cewa, an bayar da Tallafin ga Marayu, Limamai, Zawarawa, Masu Ƙananan Sana'oi, Exco, Mata, Matasa, Students, yan Media, Dagattai, Mabuƙata, yan siyasa, Ƙungiyar Teloli, Ƙungiyar Masu Shayi da Masu chajin waya, da sauran su. Inda ko wanne daga cikinsu zai amfana da Tallafin, Naira Dubu Goma (10,000)

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda PhD, yayi Jin-Jina gami da fatan Alkhairi ga Kakakin Majalissar akan wannan abin Alkhairi da yayi, sannan yayi roƙo gami da Jan hankali ga wanda suka amfana da wannan Tallafin da suyi amfani dashi ta hanyar daya dace, domin su bunƙasa Kasuwar su. 

Haka kuma Mataimakin Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar, Alh. Bala Abu Musawa, ya taya mutanen Daura murna, bisa ga Jajirtaccen Shugaba da suka samu.

Taron ya samu Halartar Tsohon Shugaban Ƙasar Nigeria, Gen. Muhammadu Buhari, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa PhD, Shugaban Jam'iyyar APC na Jiha da Mataimakinsa, Yan Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, kwamishinoni da masu bada shawara, Wakilin Mai Martaba Sarkin Daura, Hajia Ambarud Sani Wali, Shugaban karamar hukuma, Tsofaffin yan Majalissar Jiha, Barr. Ahmad Usman El-Marzuq, da sauran manyan baƙi

Kakakin Majalissa ya bayar da kyautar Sa (Bijimi) ga Muhammadu Buhari, da kyautar Doki ga Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa. 
 
Sannan Ƙungiyoyin Daura Forum, DECA, DEDA, Health and Education Department, Ƙungiyoyin Addini, da Babbar Ƙungiyar, Daura Consortium sun bayar da Lambobin Yabo da Girmamawa (Award) ga Mai Girma Kakakin Majalissar Dokoki a bisa ayyukan Alkhairin da yake aikatawa ba dare ba rana a Daura

Haka zalika Ƙungiyar Daura Forum ta bada lambar yabon ga  Muhammadu Buhari, da Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa  

Daga karshe Kakakin Majalissa yayi Godiya ga manyan baƙi da suka halarci wannan Babban taron, sannan yayi Addu'a da fatan Allah ya maida kowa gidanshi lafiya, l

Saturday, 7 January 2023

2023:Za Mu Sama Wa Katsina N10bn Daga Hasken Rana A Shekara —NNPP


Dan takarar Gwamnan Katsina a Jam’iyyar NNPP, Nura Khalil, yi alkawarin tara kudaden shiga Naira biliyan 10 daga hasken rana a duk shekara a jihar.

Injiniya Nura Khalil ya ce kudaden shigar N10bn da jihar za ta rika samu daga bangaren hasken rana zai sa ba sai ta jira daga Asusun Tarayya ba.

A gaggauta kammala masana’atar tiransfomar Najeriya —Buhari
A jawabinsa a taron fara yakin neman zabensa a Karamar Hukumar Mashi, ya ce, “Na fara da Mashi ne saboda da ita da Daurawa ta Jihar Jigawa da Kankiya bisa ga binciken da muka yi sun fi samar da hasken rana da za ta samar da lantarki ba sai an jira daga wani wuri ba.

“Za mu yi amfani da wannan hasken wutar lantarkin don sama wa jihar kudaden shigar da akalla za a samu bilyan N100 a shekara.


“Kudaden za mu yi amfani da su wajen gudanar da ayyukan gwamnati ba sai mun jira na Gwamnatin Tarayya ba.”

Ya kara da cewa idan ya ci zaben da ke tafe a watan Maris, “Muna da shirin kafa banki mallakar gwamnatin jiha wanda zai iya bayar da damar yin ajiya mai kama da shirin adashe don dai mu farfado da tattalin arzikin jihar.”

Game da matsalar tsaro, dan takarar ya ce Katsina tafi sauran jihohi hadari, amma idan NNPP ta hau mulki zai zama tarihi.

Ya kuma yi shagube ga wadanda yake zargi da sayen katinan zabe da nufin yin magudin zabe, da cewa a wannan karon karyarsu a kare.
“Ana bin mata ana sayen katunan zabensu a kan N10,000 amma a karshe sai a ba su N500.

“To a sani, babu batun magudi a wannan zaben, balle a ba wani katin wani ya je ya jefa kuri’a sama da goma,” in ji shi.

Ya zargi gwamnatin APC ta Jihar Katsina da yin watsi da fannin ilmi; inda ya ce a shekara bakwai na gwamnatin, yara 100,000 sun kasa rubuta jarabawa.

Don haka ya bukaci jama’a su zabi Jam’iyar NNPP don ta fitar da su daga kunci da rashin tsaron a jihar.
Tun da farko shugaban NNPP na jihar Katsina, Sani Liti ’Yankwani, ya ce, matsalolin satar jama’a, kisa da jahilci, sun ishi mutane hankali, saboda abin da ya kira rashin kulawar gwamnatin jihar.

A kan haka ne a ce idan aka zabi NNPP, za ta kawo karshen matsalolin musamman na rashin tsaro.

Shugaban NNPP na Kasa kuma dan takararta na shugaban kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya dan takarar Gwamnam Kano na jam’iyar, Abba Kabir Yusuf (Abba gida-gida) ya wakilta, ya ce, jam’iyy ta yi kyawawan tanade-tanaden samar da ayyukan yi da tallafin sana’o’i ga mata da matasa da kuma kawo karshen matsalar tsaro.
(AMINIYA) 


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...