Kotu Ta Bayar Da Umarnin Gurfanar Da Tukur Mamu

Wata Babbar Kotu a Jihar Kaduna, ta bayar da umarnin gurfanar mawallafin Jaridar Desert Herald, Alhaji Tukur Mamu a gaban kuliya.

Kotu ta nemi Hukumar Tsaro ta Farin Kaya reshen Jihar Kaduna (SSS) da kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami da su gaggauta gurfanar da Mamun ne tare da wasu mutum biyar.

Everton ta kori Frank Lampard
An tsaurara matakan tsaro a Legas gabanin ziyarar Buhari
Bayanai sun ce ababen zargin da kotun ta nemi a gurfanar da su bisa ga madogara ta binciken da aka yi a kansu sun hada; Tukur Mamu, Faisal Tukur Mamu, Ibrahim Hussain Tinja, Abdullahi Mashi, Mubarak Hussain Tinja da Yahaya Bello.

Da yake zartas da hukunci kan karar mai dauke da kwanan watan 15 ga Disambar 2022, Alkakin Kotun Mai Shari’a E. Andow, ya ce Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya yi tanadin bai wa duk wani wanda ake zargi ’yancin gurfanar da shi a gaban kuliya hadi da tuhume-tuhume da masu kara za su gabatar.


Umarnin kotun na zuwa ne watanni bayan da jami’an tsaron kasa da kasa na Interpol suka cafke tsohon mai shiga tsakanin gwamnati da ’yan ta’adda a kokarin kubutar da fasinjojin jirgin kasan nan na Abuja zuwa Kaduna da aka sace a watan Maris na bara.

A watan Satumbar bara ne aka kama Mamu a birnin Alkahira na kasar Masar yayin da yake jiran jirgi domin tafiya kasar Saudiyya inda zai gabatar da aikin Umrah

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki