Posts

Showing posts with the label Aminu Ado Bayero

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero Ya yi sabon Aure

Image
Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya auri mata ta biyu Hauwa'u Adamu Abdullahi Dikko a Kano ranar Juma'a. Jaridar SOLACEBASE ta rawaito cewa an gudanar da daurin auren  ne a gidan marigayi Jarman Kano Farfesa Isah Hashim da ke unguwar Nasarawa GRA a cikin babban birnin tarayya. Sannan kuma Madakin Kano Alhaji Yusuf Nabahani Ibrahim ne ya wakilci Mai Martaba Sarkin a lokacin daurin auren, yayin da Alhaji Shehu Hashim ya kasance waliyin  amarya.

Tinubu ya ziyarci Sarkin Kano tare da neman addu’a

Image
Sarkin Kano Alh Aminu Ado Bayero ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da mutunta shugabanni a lokacin zabe domin kara inganta zabe mai inganci don ci gaban kasa.  Sarkin ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Apc, Asiwaju bola Ahmad tunibu a fadarsa,  Sarkin wanda ya bayyana Kano a matsayin cibiyar zabe ya yi kira ga jama'a da su yi amfani da kwarewarsu wajen zaben wadanda suka yi shugabancesu don zama babban fa'ida ga al'umma  Tun da farko dan takarar shugaban kasar Cif Bola Ahmad Tunibu ya ce ya je jihar Kano ne domin kaddamar da yakin neman zabensa a Arewa maso Yamma kuma ya nemi addu'ar sarakuna da kuma al'ummar jihar   A yayin ziyarar dan takarar shugaban kasa Bola Ahmad Tunibu ya samu rakiyar gwamnan jihar Dr. Abdullahi umar Ganduje, da mataimakinsa Dr. Nasiru yusif Gawuna, gwamnan jihar Zamfara, Sanata barau jibrin, shugaban jam'iyyar na jiha Abdullahi Abbas, tsohon gwamnan jihar. s,

Hotuna: Bola Tinubu ya ziyarci Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero a fadarsa

Image
Tinubu ya kai ziyarar ban girma ga Sarkin Kano, inda ya nemi sanya albarka gabanin zaben Shugaban Kasa A 2023  Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Jagoranci Dan Takarar Shugabancin Kasa Na Jam'iyyar APC, Alhaji Asiwaju Bola Ahmed Tinubu. domin kai ziyara ga Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero.