Posts

Showing posts with the label TALAUCI

Gwamnan Kano Zai Kaddamar da Kashi Na Biyu Na Tallafin Abinci

Image
Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf na shirin raba buhunan hatsi da kuma baiwa matasa da mata da nakasassu tallafin kudi. A sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, ya ce, a ci gaba da kokarin gwamnatinsa na bayar da tallafi ga al’ummar jihar domin rage radadin tallafin man fetur, an kammala shirye-shiryen rabon hatsin da suka hada da shinkafa da masara a yankuna 484 dake cikin kananan hukumomi 44 na jihar. Gwamna Alh Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka a yau a wajen wani taro da shugabannin kananan hukumomin jiha da na kananan hukumomi/Secretries na hudu grassroot Mobilisation platforms (Community Re-Orientation Committee (CRC), Lafiya Jari, Kano PRO-PA da kuma Kwankwasiyya) taron da ya gudana. wanda aka gudanar a dakin taro na Coronation, gidan gwamnatin Kano. Gwamnan ya ce rabon kaso na biyu ya zama wajibi duba da irin matsalolin da mutane ke ciki sannan ya yi kira ga ayyukan rabar a mataki

Fiye da mutane 85 sun mutu a turmutsitsin rabon kudi a Yemen

Image
  Akalla mutane 85 suka mutu, wasu daruruwa kuma suka jikkata, sakamakon tirmtsitsi da aka yi yayin wani taron raba kudade da aka yi a Sanaa, babban birnin kasar kasar Yemen da ke karkashin ikon ‘yan tawayen Houthi. Ya zuwa yanzu mutane 3 aka tsare bisa zarginsu da hannu wajen haddasa tirmitsitsin da sanyin safiyar ranar Alhamis, bayan da daruruwan mutane suka taru a wata makaranta domin karbar kyautar kudin Riyal din kasar ta Yemen 5,000, kwatankwacin dalar Amurka 8 da ake bai wa mutum guda guda, a daidai lokacin da watan Ramadan mai alfarma ya zo karshe. Hotunan bidiyo sun nuna yadda mutanen da mummunan cinkoson ya rutsa da su, suka rika tsala ihu da neman ceto sakamakon kasa motsawar da suka yi, yayin da wasu tsiraru suka rika yunkurin fitar da mutanen da suka ji rauni. Wasu hotunan bidiyon kuwa, sun nuna gawarwakin wasu daga cikin wadanda tirmitsitsin ya rutsa da su ne yashe a kasa, sai kuma tarin takalma da sauran nau’ikan tufafin da aka yi watsi da su, yayin da kuma wani mai binc