Posts

Showing posts with the label Karbar Rashawa

Canjin Kudi Ya Rage Satar Mutane Da Karbar Rashawa —Malami

Image
Ministan Shari’a kuma Antoni-Janar na Tarayya, Abubakar Malami (SAN), ya bayyana cewa canjin kudi ta Babban Bankin Najeriya (CBN) ya yi ya taimaka wajen rage aikata ayyukan garkuwa da mutane. Malami, ya bayyana haka ne cikin wata hira da ya yi da Gidan Rediyon Tarayya da ke Kaduna, inda ya ce jama’a ba sa ganin nasara da tsarin ya haifar. Da yake bayyana hakan a ranar Juma’a, Malami ya ce: “Na fada muku maganar tana gaban kotu, ba za mu bijire wa kotu ba, za mu bi umarnin kotu amma muna da ’yancin fada wa kotu alfanun da tsarin ya haifar. “Idan ba ku ga amfanin tsarin ba, ya kamata kuma a gefe daya ku ga alfanunsa. “Idan wadancan gwamnonin sun bayyana wa kotu wahalar da ake sha saboda tsarin, ya kamata kuma a fahimci cewa tsarin a gefe daya yana warware wasu matsalolin. “Na ba ku misali da matsalar tsaro; Tun bayan da aka kaddamar da wannan tsarin garkuwa da mutane ya ragu. “Sannan ya rage yawan cin hanci da rashawa, don haka muna da ’yancin zuwa mu bayyana wa kotu amfanin