’Yan Bindiga Sun Sace Tsohon Kanar Din Soja A Zamfara

 


’Yan bindiga sun sace Kanar Lawal Rabiu Yandoto (mai ritaya) a kan hanyarsa ta zuwa garinsu, Yandoto da ke Karamar Hukumar Tsafe a Jihar Zamfara.

Wata majiya ta bayyana cewa ’yan bindigar sun sace shi ne tare da ’ya’yansa biyu da kuma wasu.

“Maharan sun yi wa Kanar kwanton bauna da misalin karfe 6 na yamamcin ranar Lahadi, suka sace shi tare da ’ya’yansa biyu da kuma wasu mutum biyu,”  in ji majiyar.

Majiyar ta ce an ji karar harbe-harbe daura da shiga garin na Yandoto lamarin da ya tilasta mutane guje-guje domin tsira.

Kakakin ’yan sandan jihar bai daga waya ba ballatana a ji ta bakinsa kan lamarin.

(AMINIYA)

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki