Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yace 'yan arewa basu da wanda zasu zaba sama da Bola Tinubu

 



Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce ’yan Arewa ba su da wani dalili ko kadan da zai hana su zabar dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu.

Ya ce dan takarar tasu ya yi sadaukarwa mai tarin yawa wajen bunkasa Dimokuradiyya a Najeriya, musamman wajen kokarinsa na cicciba dan Arewa ya zama Shugaban Kasa.

Saboda haka, Ganduje ya ce yanzu ne daidai lokacin da ya dace a rama wa kura aniyarta.

. https://noordakata.blogspot.com/2022/12/sojojin-haya-sun-kama-jirgi-maare-da.html

. https://noordakata.blogspot.com/2022/12/gasar-sukuwar-dawaki-ta-premier-ta.html

Ganduje ya bayyana haka ne yayin wani taro da wata kungiya mai suna Volunteers for Democracy, karkashin Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Usman Alhaji ta shirya a Kano ranar Asabar.

“A baya, ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarar ’yan Arewa, don haka ya kamata mu ma mu nuna halacci.

“Tinubu ya goyi bayan Buhari a gwagwarmayarsa har ya zama Shugaban Kasa. Bai nemi a biya shi da kowanne irin matsayi ba a gwamnati, kuma ya ci gaba da goyon bayan gwamnatin.

“Ni ban ma taba ganin masoyin ’yan Arewa ba kamar shi,” inji Ganduje

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki