El-Rufai ya yi wa fursunoni 11 afuwa a Kaduna



Gwamnan jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya Malam Nasir Ahmad El-Rufai, ya amince da yin afuwa ga fursunoni 11 daga gidajen yarin jihar domin murnar sabuwar shekarar 2023.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga gwaman kan kafofin yaɗa labarai na gwamnan jihar Mista Muyiwa Adekeye ya fitar.

Afuwar ta shafi fursunonin da suka nuna kyakkyawan hali da waÉ—anda suke fama da rashin lafiya kamar yadda sanarawar ta bayyana.

Haka kuma gwamnan ya nemi al'ummar jihar da su ci gaba da kasancewa masu son zaman lafiya, tare da fatan cewa aikin da ya faro tun a shekarar 2015 domin inganta rayukan al'umma jihar za su ci gaba a gwamnati mai zuwa.

(BBC HAUSA)

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki