Search This Blog

Thursday, 4 May 2023

Wani Yaro Ya Kashe Mahaifiyarsa A Kano

Wani karamin yaro a unguwar Rimin Kebe da ke Karamar Hukumar Nassarawa a Jihar Kano ya daba wa mahaifiyarsa wuka lamarin da ya sa ta ce ga garinku nan.

Wani ganau mazaunin yankin, Muhammad Abdu, ya shaida wa Aminiya cewa lamarin ya faru ne yayin da aka sami jayayya tsakanin marigayiyar da dan nata da ake wa lakabi da Kwarangwal.


Ya bayyana cewa, “lokacin da muka ji ihunta mun garzaya gidan don kai dauki inda muka same ta kwace cikin jini male-male ga kuma yanka a jikinta.”

A cewarsa tuni wanda ake zargi ya cika wandonsa da iska bayan ya yi aika-aikar.

Haka kuma ya bayyana cewa daga baya an garzaya da marigayiyar Asibitin Koyarwa na Muhammadu Abdullahi Wase.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis, inda ya ce zai yi karin haske akan lamarin daga bisani.
AMINIYA 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...