Za a ci gaba da amfani da tsofaffin kudi —Tinubu

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa za a ci gaba da amfani da tsoffin kudin da gwamnatin Buhari ta soke.

Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta yi gyaran fuska ga dokar sauyin kudi da gwamnatin Buhari ta yi.
Tinubu wanda ya bayyana hakan bayan an rantsar da shi, ya ce gwamnatinsa za ta yi gyaran fuska ga dokar haraji, domin saukaka wa ’yan kasuwa gudanar da harkokinsu domin samun sauki da nufin bunkasa bangaren.

Tinubu ya soke biyan tallafin mai
Shugaban Kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya janye tallafin man fetur.

Tinubu ya ce tallafin mai ya zama tarihi ne jim kadan bayan an ranstar da shi a Dandalin Eagle Square da ke Abuja.

Ya ce biyan tallafin abu ne ba mai dorewa ba, don haka gara a yi amfani da kudaden da ake kashewa wajen biyan tallafin domin yin wasu ayyukan raya kasa.

AMINIYA 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki