Search This Blog

Saturday, 20 May 2023

Labari Da Dumiduminsa: Tawagar Farko Ta Maniyyatan Kasar Pakistan Mai Dauke Da Mutum 138 Sun Sauka A Makkah

Kashi na farko na jigilar alhazan Pakistan ya isa Makkah domin kammala shirye-shiryen mahajjatan Pakistan.

Wakilin Rediyon Pakistan Javed Iqbal ya ruwaito daga Makkah cewa rukunin mutane 138 sun hada da Moavineen 19, kwararrun likitoci 67 da kuma jami’an ma’aikata 52 na ma’aikatar kula da harkokin addini.

Tawagar za ta kafa sansanonin kula da lafiya tare da kammala wasu shirye-shirye da suka hada da wurin kwana, sufuri da kuma wuraren cin abinci ga alhazan Pakistan.

Yana da kyau a ambaci cewa aikin jigilar alhazai na Pakistan zai fara aiki daga gobe.

Bayan shekarar 2019, wannan shi ne aikin Hajji na farko mai cikakken karfi wanda a karkashinsa kimanin alhazan Pakistan 180,000 ne za su tafi kasar Saudiyya don sauke farali.

A bisa umarnin na musamman na ministan harkokin addini Talha Mahmood, ma'aikatan ma'aikatar suna yin kokari sosai don ganin aikin Hajjin bana ya samu nasara.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...