Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin shugaban da sakataren zartarwa da mambobin hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano.
A sanarwar da babban sakataren yada labaran gwamnan ya sanyawa hannu, tace wadanda aka nada sune:
1. Alhaji Yusuf Lawan
Shugaba
2. Alhaji Laminu Rabi’u
Sakataren Zartarwa
3. Sheikh Abbas Abubakar Daneji - Mamba
4. Shiek Shehi Shehi Maihula- Mamba
5. Amb. Munir Lawan- Mamba
6. Shiek Isma'il Mangu, Memba
7. Hajiya Aishatu Munir Matawalle- Mamba
8. Dr. Sani Ashir- Mamba
Ana sa ran wadanda aka nada za su karbe al’amuran hukumar nan take domin ganin an samu nasarar gudanar da aikin Hajjin 2023.