Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Sake Sanar Da Nadin Sabbin Mukamai A Gwamnanatina

Gwamnan Jihar Kano Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da karin mukamai biyar a mukamai daban-daban.

A cewar sanarwar da babban sakataren yada labaran gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, ta ce wadanda aka nada sune kamar haka.

1. Injiniya Garba Ahmed Bichi
Manajan Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Kano

2. Dr. Rahila Mukhtar
Babban Sakataren Hukumar Kula da Gudunmawar Kiwon Lafiya ta Jihar Kano (KCHMA).

3. Hassan Baba Danbaffa
Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tituna ta Jihar Kano (KARMA).

4. Arc. Ibrahim Yakubu
Manajan Daraktan hukumar tsara Birane ta Jihar Kano (KNUPDA).

5. Abdulkadir Abdussalam
Akanta Janar na Jihar Kano

Nan ba da jimawa ba za a sanar da bikin rantsar da wadanda aka nada domin ba su damar sauke nauyin da aka dora musu nan take.



Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki