Gwamna Ganduje ya mika takardun bayar da mulki ga Dr Abdullahi Baffa Bichi

Da yake mika takardun a gidan gwamnati Alhaji Usman Alhaji ya yi nuni da cewa kwamitocin biyu suna da kyakkyawar alakar aiki yayin da suka yi musayar shirye-shirye kan yadda za a gudanar da muhimmin taron don tabbatar da mika mulki cikin sauki.

Ya bayyana cewa kwamitocin duka suna aiki ne don maslahar al’ummar Kano.

Alhaji Usman Alhaji ya yi nuni da cewa mika wuya ga gwamnati mai zuwa zai amfanar da su wajen ci gaba da yi wa al’ummar Kano hidima.

Ya kara da cewa takardun sun cika kuma suna dauke da dukkanin bayanan da ake bukata 

A nasa bangaren shugaban kwamitin Karbar Mulki na gwamnati mai jiran gado, Dr Abdullahi Baffa Bichi ya nuna godiya ga kwamitin mika mulki na jihar Kano bisa kyakkyawan aikin da aka yi wajen hada takardun mika mulki.

Ya ba da tabbacin cewa a matsayinsu na yan kwamiti,  za su duba takardun sosai kafin su mika su ga zababben gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf.

Ya yi amfani da taron wajen yaba wa kwamitin gwamnati bisa aikin da aka yi da kuma ci gaba da hadin gwiwa a wannan fanni.

Daga cikin muhimman abubuwan da suka faru a taron sun hada da gabatar da mika takardun 


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki