Yanzu-yanzu: Gwamnan jihar Kano ya sanar da nadin sabbin mukamai

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf na fatan bayyana wadannan nadi.

1. Hon. Shehu Wada Sagagi, Shugaban Ma’aikata

2. Dr Abdullahi Baffa Bichi, sakataren gwamnatin jiha 

3. Dr. Farouq Kurawa
Babban Sakatare Gwamna 

4. Hon. Abdullahi Ibrahim Rogo, babban mai lura da Karbar baki

5. Sanusi Bature Dawakin Tofa, Babban Sakataren Yada Labarai

A cewar babban sakataren yada labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, Wadannan nade-naden sun fara aiki ne daga yau Litinin 29 ga Mayu, 2023. An zabi wadanda aka nada ne bisa la’akari da tarihinsu, sadaukarwa da amincin su.


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki