Search This Blog

Sunday, 14 May 2023

#Hajj2023 : Hukumar Alhazai Ta Kano Za Ta Fara Gudanar Da Aikin Duba Lafiyar Maniyyatanta

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta jihar kano ta sanar da cewa gobe litinin za ta fara duba lafiyar alhazan da suka shirya zuwa aikin hajjin bana.

Mataimakiyar daraktar fadakarwa ta hukumar, Hadiza Abbas Sanusi ce ta bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Lahadi.

Ta ce za a gudanar da gwajin lafiyar a cibiyoyin kiwon lafiyar jihar daga ranar Litinin, 14 ga Mayu.

Ta sanar da cewa kowane mahajjaci ya karbi fom din tantance lafiyarsa daga wakilinsa a kananan hukumominsu inda aka biya kudin aikin Hajjin.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...