Gwamnan Jihar Neja, Ya Nada Sarkin Borgu A Matsayin Amirul Hajj

Gwamnan jihar Neja, Alhaji Abubakar Sani Bello, ya nada Sarkin Borgu Alhaji Mohammed Sani na shida a matsayin Amirul Hajj na jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Neja Alhaji Ibrahim Matane ya fitar.

Sauran mambobin tawagar Amirul Hajj a cewar Sakataren Gwamnatin sun hada da Injiniya Mohammed Suleiman da Alhaji Shehu Yahaya da Yarima Musah Madami a matsayin Sakatare.

Sakataren Zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Neja, Alhaji Muhammad Awwal, wanda ya taya Amirul Hajji murna, ya tabbatar musu da cewa hukumar za ta baiwa Amirul Hajj da sauran ‘yan tawagar cikakken goyon baya wajen ganin an samu nasarar aikin Hajjin 2023. .

Sakataren zartarwar ya ci gaba da cewa, an kammala dukkan shirye-shiryen fara aikin Hajji na bana a Jahar 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki