Hajj2023: Duk Karin Da Aka Samu A Kudin Aikin Hajin Bana, Babu Maniyyacin Da Za Ce Ya Sake Biya- Shugaban NAHCON


Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) ta bayyana cewa, duk da karin dalar Amurka kusan $313 (N141, 476) kan kudin aikin hajjin bana, hukumar ba za ta nemi maniyyatan su sake biyan wasu kudade ba.

Shugaban Hukumar NAHCON, Zikirullah Kunle Hassan, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabin bude taron bita na yini daya ga jami’an Hajji da ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta shirya, wanda aka gudanar a gidan Hajji da ke Abuja a ranar Asabar din da ta gabata bayan barkewar rikici a kasar Sudan da kuma ‘yan gudun hijira. rufe sararin samaniyarsa, kamfanonin jiragen saman Najeriya hudu da aka zaba don aikin Hajjin 2023 sun bukaci hukumar da ta ba ta dala 250 tikitin jirgin kowane mahajjaci.

 

Alhaji Hassan ya kuma ce hukumar a ranar 6 ga watan Mayu, ta gano cewa akwai ƙarin kudaden aiki guda biyu na dalar Amurka 63 daga Saudi Arabiya wanda ba a sanyasu ba a tattaunawar da aka yi tun farko gabanin sanar da farashin farashi na ƙarshe.

Ya ce tuni NAHCON ta rubutawa ma’aikatar aikin Hajji cewa an samu karin, inda ya kara da cewa, “muna fatan samun amsa mai kyau”.

Shugaban NAHCON ya ci gaba da cewa hukumar ta yanke shawarar ba za ta kara wannan nauyi a kan maniyyatan mu ba.

Alhaji Hassan ya ce a yanzu NAHCON kungiya ce mai dogaro da kanta wadda ba ta samun tallafin gwamnati, maimakon haka ya ce hukumar na samar da kudaden shiga ga gwamnati.

IHR

 

 


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki