Hajj2023 - Hukumar Alhazai Ta Kano Za Ta Fara Aikin Gwajin Juna Biyu Ga Maniyyata Mata

Hukumar kula Jin dadin alhazai ta Jihar Kano, na sanar da Maniyyata Mata na Jihar Kano cewa za'a fara Gwajin Juna-biyu wato ( Scanning ) ga Maniyyata Mata 

Matan da za a fara dasu a gobe Lahadi 21 ga watan Mayu 2023, kamar yadda sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin Ilmantarwa da hulda da jama’a ta hukumar Hajiya Hadiza Abbas Sanusi ta rabawa manema labarai, sun hada da na kananan hukumomin Takai, Sumaila, Garko, Albasu, Tudun wada, Bebeji, Doguwa da Karamar Hukumar Garun Malan

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa za a gudanar da aikin a Sansanin alhazai na Jihar Kano wato Hajjcamp da misalin karfe Tara na safe

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki