Bola Tinubu Ya Bar Najeriya Zuwa Turai Domin Ziyarar Aiki

A yammacin Larabar nan ne zababben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bar Najeriya zuwa kasashen Turai domin ziyarar aiki.

A sanarwar da daya daga masu hidima masa a fannin yada labarai, Tunde Rahman ya fitar, ta ce Zai yi amfani da damar tafiya don daidaita tsare-tsare da shirye-shiryen mika mulki, da zabin manufofinsa tare da wasu manyan mataimakansa ba tare da matsananciyar wahala da damuwa ba.

A yayin ziyarar, zababben shugaban kasar zai tattauna da masu zuba jari da sauran manyan abokan hulda da nufin tallata guraben zuba jari a kasar da kuma shirye-shiryen gwamnatinsa na samar da yanayi mai kyau na kasuwanci ta hanyar manufofi da ka'idoji.
 

Asiwaju Tinubu na fatan gamsar da su kan shirin Najeriya na yin kasuwanci a karkashin jagorancinsa ta hanyar hadin gwiwar da za ta amfana da juna kan samar da ayyukan yi da kuma samun kwarewa.
 
Farfado da tattalin arzikin kasar ya zama wani babban ginshiki na ajandar sabunta fata na Tinubu kuma taron na daya daga cikin kokarinsa na sake farfado da martabar Najeriya a tsarin tattalin arzikin duniya da samar da damammaki ga dimbin matasan kasar.
 
Ya zuwa yanzu dai zababben shugaban kasar ya yi alkawarin zai kai ga gaci kuma ziyarar na nuni da jajircewarsa kan wannan alkawari domin tuni ya fara tattaunawa da masu ruwa da tsaki na duniya kan muhimman batutuwan da suka shafi tattalin arziki da tsaro.

Kafin ya bar kasar, Asiwaju Tinubu ya gana da ‘yan takarar majalisar wakilai da ‘yan takarar shugaban kasa da mataimakinsa wanda jam’iyyarsa ta APC ta amince da shi. Tajudeen Abbas and Hon. Benjamin Kalu, wanda kungiyar hadin gwiwa ta majalisar ta gabatar masa.

An shirya zai dawo nan ba da jimawa ba don shirye-shiryen rantsar da shi a hukumance a matsayin shugaban kasar na 16 a ranar 29 ga Mayu, 2023.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki