Wani dan ta'adda ya tarwatsa kansa da bam a Kaduna

 


Jama'a sun shiga firgici a jihar Kaduna ta Najeriya bayan wani mutun da ake zargin dan ta'adda ne ya tarwatsa kansa da bam a daidai lokacin da jami'an tsaro ke kokarin cafke shi, yayin da gawarsa ta yi kaca-kaca.

Lamarin ya faru ne a kan hanyar Ibrahim Haske da ke unguwar Keke a Millenium City a sanyin Safiyar wannan Litinin. 

Mutanen da lamarin ya auku a kan idanunsu sun ce, an yi jin karar harbe-harben bindiga da misalin karfe 1 na cikin daren da ya gabata lokacin da jami'an tsaron farin kaya na DSS da sojoji suka dirar wa gidan dan ta'addar da ake zargi.

Mutumin ya tarwatsa kansa ne da bam din bayan ya fahimci cewa, jami'an tsaron sun yi masa zobe.

Rahotanni sun ce, mutumin ya dauki lokaci yana musayar wuta tsakaninsa da jami'an tsaro kafin yanke shawarar kashe kansa da kansa, yayin da aka gano bindiga kirar AK-47 a cikin gidansa da kuma wasu bama-bamai.

PUBLICITÉ

Tuni jami'an tsaro suka tafi da matar mutumin da 'ya'yansa bayan ya kashe kansa.

RFI

.

 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki