Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Nada Dr Ahmad Jinjiri Kiru A Matsayin Babban Mataimaka Masa A Harkokin Majalisa

Zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Kiru da Bebeji a jihar Kano  Abdulmumin Jibrin Kofa ya amince da nadin Dr Ahmad Jinjiri Kiru a matsayin babban mai taimaka masa a majalisar tarayya (SLA). 

Dr Jinjiri fitaccen dan Kwankwasiyya ne wanda ya amfana da shirin karo karatu da aka yi 

Yana da digirin digirgir (PhD) a fannin harkar Akanta tare da gogewar shekaru a fannin Ilimi, jama'a da kuma kamfanoni masu zaman kansu.

A wani ci gaban kuma Abdulmumin Jibrin Kofa ya sake nada wasu karin mutum 3 mukamai dadan-daban

Wadanda aka nada sun hada da :

1. Ashiru Dankaka Bebeji a matsayin mai taimaka masa kan harkokin majalisa (LA)

2. Bashir Bala Bashir Mai Taimaka masa kan harkokin yada Labarai

3. Umar Ahmad a matsayin Mai daukar hoto.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki