Search This Blog

Friday, 28 April 2023

Firaministan Pakistan ya tsallake rijiya da baya

 


Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif ya tsallake rijiya da baya, bayan da ‘yan majalisar kasar suka kada kuri’ar yanke kauna, yayin da sauran kungiyoyin fararen hula suka matsa kan a fara shirin gudanar da babban zaben kasar. 

Sharif ya sami kuri’un amincewa guda 180, yayin da ‘yan majalisa 172 suka nuna rashin amincewa da salon shugabancin sa, abinda ya bashi damar ci gaba da rike mukamin sa da kyar. 

Ko da yake jawabi, kakakin majalisar dokokin kasar Raja Pervais Asharf, yace a yanzu abinda majalisar zata mayar da hankakli shine batun babban zaben da ke tafe. 

Sharif wanda ya gaji Imran Khan ya yabawa mambobin jam’iyyyar sa da ke majalisar bayan da suka amince da salón mulkin sa, tare da yanke hukuncin sake bashi dama, ta hanyar kada kuri’ar amincewa da shi. 

rfi

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...