Gwamnati ta karrama limamin da ya tausasa kyanwa a Salla

 


Gwamnatin Algeria ta karrama limamin nan, Imam Walid Mehsas wanda kyanwa ta dare jinkinsa a daidai lokacin da yake jagorantar Sallar Taraweeh, inda cikin tausasawa ya yi ta shafar kwanyar wadda ta sunbace shi kafin daga bisani ta sauka daga jikinsa don ratsin kanta.

Wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta ne ya nuna yadda Imam Walid ya mu’amalanci kwanyar cikin kyawun yanayi, lamarin da ya kayatar da jama’a da dama hatta wadanda ba Musulmai ba daga sassan duniya.

Limamin ya sha yabo da jinjina, yayin da manyan kafafen yada labarai na duniya suka yi ta yada wannan labarin.

Yanzu haka gwamnatin Algeria ta gayyace shi tare da shirya masa taron liyafa na musamman, inda Ministan Kula da Lamurran Addini na Kasar, Dr. Youssaf Belmahdi ya yaba masa kan wannan kyakkyawar dabi’ar da ya nuna wa dabba.

RFI

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki