Kujerar Dan Majalisa: Ban Gamsu Da Nasarar NNPP Ba, Zan Tafi Kotu – Dan Ganduje


 Umar Abdullahi Gandujedan Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, wanda ya tsaya takarar dan Majalisar Wakilai a jam’iyyar APC, ya ce bai yarda da sakamakon zaben da ya ba NNPP nasara ba.

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) dai ta ayyana Injiniya Tijjani Abdulkadir Jobe a matsayin wanda ya lashe kujerar dan majalisar a mazabar Dawakin Tofa/Tofa/Rimin Gado, a jam’iyyar NNPP.

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa, Tuni dai Umar, wanda aka fi sani da Abba Ganduje ya maka Tijjani Jobe a gaban kotun sauraron kararrakin zabe.

Abba, ta bakin lauyansa, Barista A.T Falola, ya kuma kalubalanci INEC kan ayyana Jobe a matsayin dan takarar da ya samu rinjayen kuri’un da aka kada a lokacin zaben.

Da ya ke gabatar da kara a gaban kotun, Falola ya roki kotun da ta gudanar da shari’ar a kan Jobe da kuma jam’iyarsa ta NNPP mai sakatariya a unguwar Sharada a Kano

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki